< Hosiya 14 >

1 Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
Israël, retourne-toi jusqu'à l'Eternel ton Dieu; car tu es tombé par ton iniquité.
2 Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
Prenez avec vous ce que vous avez à dire, et retournez-vous à l'Eternel, et lui dites: Ote toute l'iniquité, et prends le bien, [pour le mettre en sa place], et nous [te] rendrons les bouveaux de nos lèvres.
3 Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
L'Assyrie ne nous délivrera pas; nous ne monterons plus sur des chevaux, et nous ne dirons plus à l'ouvrage de nos mains: [Vous êtes] nos dieux; car l'orphelin trouve compassion devant toi.
4 “Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
Je guérirai leur rébellion, et les aimerai volontairement; parce que ma colère est détournée d'eux.
5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
Je serai comme une rosée à Israël; il fleurira comme le lis, et jettera ses racines comme [les arbres] du Liban.
6 tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
Ses branches s'avanceront, et sa magnificence sera comme celle de l'olivier, et son odeur comme celle du Liban.
7 Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
Ils retourneront pour se tenir assis sous son ombre, et ils foisonneront [comme] le froment, et fleuriront comme la vigne, et l'odeur de chacun d'eux sera comme celle du vin du Liban.
8 Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
Ephraïm [dira]: Qu'ai-je plus à faire avec les faux dieux? Je l'exaucerai, et le regarderai; je lui serai comme le sapin vert, ton fruit procédera de moi.
9 Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.
Qui est celui qui est sage? qu'il entende ces choses; et qui est celui qui est prudent? qu'il les connaisse; car les voies de l'Eternel sont droites; aussi les justes y marcheront, mais les rebelles y tomberont.

< Hosiya 14 >