< Hosiya 14 >

1 Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
[You people of] Israel, return to Yahweh our God. You are being punished because of the sins which you have committed.
2 Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
So now return to Yahweh and say [MTY] this to him: “Forgive us for all the sins that we have committed, and kindly accept (us/our sacrifices) in order that we may thank/praise you [IDM].
3 Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
[We admit that] Assyria will not save us, and our war horses will not save us, either. We will never again say, ‘You are our gods’ to [the idols that] we [SYN] have made. You are the one who acts mercifully to orphans.”
4 “Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
[Yahweh says, “If they say that to me, ] I will forgive them for having (turned away from/abandoned) me, and I will love them with all my inner being, because I [PRS] will have stopped being angry with them.
5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
I will be to the people of Israel like dew [that refreshes the soil]. When I do that, they will [become as delightful as] [MET] lilies are when they are blooming. [No one will be able to conquer them; ] they will be [as unmovable as] [SIM] the roots [of cedar trees].
6 tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
[Their good influence will spread] like [MET] the branches of a tree. They will be like [SIM] beautiful olive trees, and [they will be as delightful as] [SIM] the aroma of the cedar [trees in] Lebanon.
7 Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
People will [come to them to be protected] [like people are protected from the hot sun by being] [MET] in the shade [of a tree]. They [will (flourish/be strong) like] [SIM] grain that grows well. They will [be successful like] a vineyard [in which grapes grow abundantly]. They will become as famous/well-known as [SIM] the wines from Lebanon.
8 Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
[You people of] Israel, do not [RHQ] have anything more to do with idols; if you [get rid of your idols], I will answer your [prayers] and take care of you. I am like [MET] a strong/green pine tree, and your blessings come from me.”
9 Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.
Those who are wise will understand the things [about which I have written]. Those who think well will pay careful attention to them. The things that Yahweh wants us to do [MET] are right; righteous people will conduct their lives adhering to them. But those who rebel against Yahweh will be ruined.

< Hosiya 14 >