< Hosiya 14 >

1 Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
Israel, return to the LORD your God; for you have fallen because of your sin.
2 Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
Take words with you, and return to the LORD. Tell him, "Forgive all our sins, and accept that which is good, and we will offer the fruit of our lips.
3 Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
Assyria can't save us. We won't ride on horses; neither will we say any more to the work of our hands, 'Our gods.' for in you the fatherless finds mercy."
4 “Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
"I will heal their waywardness. I will love them freely; for my anger is turned away from him.
5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
I will be like the dew to Israel. He will blossom like the lily, and send down his roots like Lebanon.
6 tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
His branches will spread, and his beauty will be like the olive tree, and his fragrance like Lebanon.
7 Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
They will return and dwell in his shade. They will live and be abundantly satisfied with grain, and blossom like the vine. Their fragrance will be like the wine of Lebanon.
8 Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
Ephraim, what have I to do any more with idols? I answer, and will take care of him. I am like a green fir tree; from me your fruit is found."
9 Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.
Who is wise, that he may understand these things? Who is prudent, that he may know them? For the ways of the LORD are right, and the righteous walk in them; But the rebellious stumble in them.

< Hosiya 14 >