< Hosiya 14 >
1 Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
Return, O Israel, even unto the Lord thy God; for thou hast stumbled through thy iniquity.
2 Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
Take with you swords, and return to the Lord: say unto him, “Pardon all [our] iniquity, and accept [our return to] good; and let us repay the steers [of sacrifice] with [the prayer of] our lips.
3 Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
Asshur shall not help us; upon horses will we not ride: and we will no more say, Ye are our gods, to the work of our hands; for in thee alone the fatherless obtaineth mercy.”
4 “Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
I will heal their backsliding, I will love them freely; for my anger is turned away from them.
5 Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
I will be as the dew unto Israel: he shall bloom as the lily; and he shall strike his roots as [the forests of] Lebanon.
6 tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
His suckers shall spread out, and his beauty shall be as that of the olive-tree, and his smell as that of the Lebanon.
7 Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
They shall return that sat under his shade; they shall revive as corn, and bloom as the vine: the scent of which shall be as that of the wine of Lebanon.
8 Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
Ephraim [shall say], What have I to do any more with idols? I have answered, and will observe him; I will be [to him] like a green fir-tree; through me is thy fruit found.
9 Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.
Who is wise, that he may understand these things? intelligent, that he may know them? for righteous are the ways of the Lord; and the just shall walk in them; but the transgressors will stumble through them.