< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
هنگامی که افرایم به لرزه سخن گفت، خویشتن را در اسرائیل مرتفع نمود؛ اماچون در امر بعل مجرم شد، بمرد.۱
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
و الان گناهان می‌افزایند و از نقره خود بتهای ریخته شده وتماثیل موافق عقل خود می‌سازند که همه آنهاعمل صنعتگران می‌باشد و درباره آنها می‌گویندکه اشخاصی که قربانی می‌گذرانند گوساله‌ها راببوسند.۲
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
بنابراین، ایشان مثل ابرهای صبح ومانند شبنمی که بزودی می‌گذرد، هستند. و مثل کاه که از خرمن پراکنده شود و مانند دود که ازروزن برآید.۳
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
اما من از زمین مصر (تا حال ) یهوه خدای توهستم و غیر از من خدای دیگر را نمی شناسی وسوای من نجات‌دهنده‌ای نیست.۴
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
من تو را دربیابان در زمین بسیار خشک شناختم.۵
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
چون چریدند، سیر شدند و چون سیر شدند، دل ایشان مغرور گردید و از این جهت مرا فراموش کردند.۶
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
پس من برای ایشان مثل شیر خواهم بود و مانندپلنگ به‌سر راه در کمین خواهم نشست.۷
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
و مثل خرسی که بچه هایش را از وی ربوده باشد، بر ایشان حمله خواهم آورد و پرده دل ایشان راخواهم درید و مثل شیر ایشان را در آنجاخواهم خورد و حیوانات صحرا ایشان راخواهند درید.۸
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
‌ای اسرائیل هلاک شدی، اما معاونت تو بامن است.۹
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
الان پادشاه تو کجاست تا تو را درتمامی شهرهایت معاونت کند و داورانت (کجایند) که درباره آنها گفتی پادشاه و سروران به من بده؟۱۰
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
از غضب خود، پادشاهی به تو دادم واز خشم خویش او را برداشتم.۱۱
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
عصیان افرایم بسته شده و گناه او مخزون گردیده است.۱۲
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
دردهای زه مثل زنی که می‌زاید بروی آمده است و او پسری نادانشمند است زیرا در وقتش، در جای تولد فرزندان نمی ایستد.۱۳
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
من ایشان را از دست هاویه فدیه خواهم داد و ایشان را از موت نجات خواهم بخشید. ای موت ضربات تو کجاست و‌ای هاویه هلاکت تو کجا است؟ پشیمانی از چشمان من مستور شده است. (Sheol h7585)۱۴
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
اگر‌چه در میان برادرانش ثمر آورد، اما باد شرقی می‌وزد وباد خداوند از بیابان برمی آید و منبع اوخشک می‌گردد و چشمه‌اش می‌خشکد و اوگنج تمامی اسباب نفیسه وی را تاراج می‌نماید.۱۵
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
سامره متحمل گناه خود خواهدشد، زیرا به خدای خود فتنه انگیخته است. ایشان به شمشیر خواهند افتاد و اطفال ایشان خرد و زنان حامله ایشان شکم دریده خواهندشد.۱۶

< Hosiya 13 >