< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
Lapho u-Efrayimi ekhuluma, abantu bathuthumela; wabatshazwa ko-Israyeli. Kodwa waba lecala lokukhonza uBhali wasesifa.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
Khathesi benza izono njalonjalo; bazenzela izithombe ngesiliva sabo, izifanekiso ezenziwe ngokuhlakanipha, zonke ziyimisebenzi yezingcitshi. Ngabantu laba kuthiwa, “Banikela imihlatshelo yabantu, bange izithombe zamathole.”
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Ngakho bazakuba njengenkungu yekuseni, njengamazolo ekuseni anyamalalayo, njengamakhoba asuka ezizeni, njengentuthu iphuma ewindini.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
“Kodwa mina nginguThixo uNkulunkulu wenu, owalikhupha elizweni laseGibhithe. Kaliyikwamukela omunye uNkulunkulu ngaphandle kwami, hatshi omunye uMsindisi ngaphandle kwami.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
Ngalilondoloza enkangala, elizweni elilokutshisa okuvuthayo.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
Lapho ngibapha ukudla, basutha; sebesuthi, basuka bazigqaja; basebengikhohlwa.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
Ngizakwehlela phezu kwabo njengesilwane, ngizacathama ngasendleleni njengengwe.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Njengebhele elithathelwe imidlwane yalo ngizabahlasela ngibaqhaqhe. Ngizabadla njengesilwane, inyamazana yeganga izabadabula.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
Uchithiwe, wena Israyeli, ngoba umelane lami, umelane lomsizi wakho.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Ingaphi inkosi yakho, ukuba ikusize na? Bangaphi ababusi bakho kuwo wonke amadolobho akho, bona owathi ngabo, ‘Ngipha inkosi lababusi’?
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
Ngakho ngakunika inkosi ngithukuthele, njalo ngolaka lwami ngayisusa.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
Icala lika-Efrayimi ligciniwe, izono zakhe zigcinwe emibhalweni.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
Ufikelwa yibuhlungu obunjengowesifazane ehelelwa, kodwa ungumntwana ongelalwazi; lapho isikhathi sifika, kabuyi ekuvulekeni kwesizalo.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
Ngizabahlenga emandleni engcwaba; ngizabasindisa ekufeni. Zingaphi, we kufa izifo zakho? Kungaphi, we ngcwaba, ukuchitha kwakho? Kangiyikuba lesihawu, (Sheol h7585)
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
lanxa ekhula phakathi kwabafowabo. Umoya wasempumalanga ovela kuThixo uzafika, uphephetha uvela enkangala; intwasa yakhe izakwehluleka, lemithombo yakhe itshe. Indlu yakhe yokugcinela izaphangwa yonke ingcebo yayo.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Abantu baseSamariya kuzamela balithwale icala labo, ngoba bamhlamukele uNkulunkulu wabo. Bazabulawa ngenkemba; insane zabo zizasakazelwa phansi, abesifazane babo abazithweleyo baqhaqhwe.”

< Hosiya 13 >