< Hosiya 13 >
1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
Dès qu’Ephraïm parlait, on tremblait; il s’éleva en Israël. Mais il se rendit coupable par Baal, et il mourut.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
Et maintenant, ils continuent à pécher; de leur argent ils ont fait une statue de fonte, des idoles selon leur idée: œuvre d’artisans que tout cela! On dit d’eux: « Sacrificateurs d’hommes, ils baisent des veaux! »
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
C’est pourquoi ils seront comme une nuée du matin, et comme la rosée matinale qui se dissipe, comme la balle que le vent emporte de l’aire, et comme la fumée qui s’en va par la fenêtre.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
Et moi, je suis Yahweh, ton Dieu, depuis le pays d’Égypte; tu ne connaîtras pas d’autre Dieu que moi, et en dehors de moi il n’y a pas de Sauveur.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
Je t’ai connu dans le désert, dans le pays de la sécheresse.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
Quand ils ont eu leur pâture, ils se sont rassasiés; ils se sont rassasiés, et leur cœur s’est élevé, et à cause de cela ils m’ont oublié.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
Je serai pour eux comme un lion, comme une panthère, je les guetterai au bord du chemin.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Je fondrai sur eux comme l’ourse privée de ses petits; je déchirerai l’enveloppe de leur cœur, et je les dévorerai là comme une lionne; la bête des champs les mettra en pièces.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
Ce qui te perd. Israël, c’est que tu es contre moi, contre celui qui est ton secours.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Où donc est ton roi, pour qu’il te sauve dans toutes les villes? Et où sont tes juges dont tu as dit: « Donne-moi un roi et des princes? »
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
Je te donne un roi dans ma colère, je te le prendrai dans ma fureur.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
L’iniquité d’Ephraïm est liée, son péché est mis en réserve.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
Les douleurs de l’enfantement viennent pour lui; c’est un enfant dénué de sagesse; car, le moment venu, il ne se présente pas pour naître.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
Je les délivrerai de la puissance du schéol, je les rachèterai de la mort. Où est ta peste, ô mort? Où est ta destruction, ô schéol? Le repentir est caché à mes yeux. (Sheol )
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Car Ephraïm fructifiera au milieu de ses frères! mais le vent d’orient viendra; le souffle de Yahweh montera du désert; sa source se desséchera, sa fontaine tarira; il pillera les trésors de tous les objets précieux.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Samarie sera punie, car elle s’est révoltée contre son Dieu; ils tomberont par l’épée! Leurs petits enfants seront écrasés, et l’on fendra le ventre de leurs femmes enceintes.