< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
[Previously], when [the leaders of] Israel spoke, the people trembled; those leaders were highly respected by the Israeli people. But the people sinned greatly by [worshiping] Baal, so now they will be killed [by their enemies].
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
Now they sin more and more; they make idols for themselves [and coat the idols] with their silver. Those idols are statues that are very cleverly made, but those statues are made by [mere] humans. But [the people are told], “Kiss those idols [that resemble a] calf, and offer sacrifices to them!”
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Therefore, those people will [disappear quickly] like [SIM] the morning mist or the dew that lies [on the ground] early [in the morning]; [they will disappear] like [SIM] chaff that is blown away from where [the wheat] is threshed, like [SIM] smoke that goes out of a chimney.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
But [Yahweh says to his people], “I am Yahweh, your God, [the one who brought your ancestors] out of Egypt. You must believe that only I am God and that there is no other God, and that there is no one else who can save you!
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
I took care of your [ancestors when they were] in the desert, where it was extremely [hot and] dry.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
When I provided food for them, their [stomachs] were full, and they were satisfied. But then they became proud and they forgot [about] me, [and you are like your ancestors]!
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
So I will attack you like [SIM] a lion [attacks other animals]; I will be like [SIM] a leopard that waits beside the road [to attack another animal].
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Like [SIM] a female bear attacks anyone that steals her cubs, I will attack you Israelis and rip you open. I will completely destroy you like [SIM] lions or [other] wild animals tear apart the animals that they catch and devour them.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
[You people of] Israel, you will be destroyed because you oppose me, the only one who (can help/helps) you.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
You have a king; (why is he [unable to save you]?/but he is [unable to save you].) [RHQ] You have [RHQ] rulers in all your towns, but they are not helping you, [either]. Your [ancestors] said, ‘Appoint for us a king and [other] leaders [to rule over us] [like the other nations have]!’
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
I was angry with them [for requesting that], but I appointed a king [to rule over] them. But [later] I became very angry with them [again], so I took their king away.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
[I have written on a scroll] a record of the sins that have been committed by you people of Israel, and I have stored away that record.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
You people are not wise; and now [you are helpless]. You are like [MET] a woman who is having birth pains but who is unable to give birth to the baby.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
I certainly will not [RHQ] save you from being killed and from going to the place where the dead people are. I will [RHQ] cause you to be afflicted by plagues and to die and be buried in graves. I will not be merciful [to you]. (Sheol h7585)
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Even if you people of Israel prosper more than the nearby nations do, [the army of Assyria] will come [like] [MET] an east wind that blows from the desert; the springs and wells in Israel will become dry; and [your enemies] will take away all your valuable possessions.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
[You people of] Samaria must be punished because you have rebelled against [me], your God. You will be killed by [your enemies’] swords; your little children will be [killed by being] dashed/thrown to the ground; the [bellies of] women [among you] will be ripped open.”

< Hosiya 13 >