< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
When Ephraim used to speak there was trembling; a prince was he in Israel. But he incurred guilt through Baal and died.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
And now they go on sinning. They make for themselves molten gods – idols of silver, skilfully made, wholly the work of smiths. Yet to such they sacrifice! And they who sacrifice kiss calf idols!
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Therefore they will be like the morning mist, like the dew that early disappears, like the chaff which blows away from the threshing floor, like the smoke from the window.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
Yet it was I, the Lord your God, ever since the land of Egypt, you know no other god but me, nor has there been any saviour except me.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
It was I who shepherded you in the wilderness, in the land of burning heat.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
When they were pastured they became full, when they were full their hearts became proud. Therefore they forgot me!
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
So now I will be to them like a lion, like a leopard will I lay in wait by the path.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
I will fall upon them like a bear robbed of her cubs, I will tear open their chests, like a lion will devour them, and like a wild beast will tear them in pieces.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
You are destroyed, Israel, by me, your only helper.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
I want to rule you! Where are your princes in your cities, those of whom you demanded, ‘Give me kings and princes.’
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
I give you kings in my anger, and take them away in my wrath.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
Ephrahn’s iniquity is gathered up, his sin is laid by in store.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
The pangs of childbirth come upon him, but he is an unwise child. For this is no time to refuse to leave the womb!
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
Should I deliver them from the power of Sheol? Should I redeem them from death? Death, where are your plagues? Sheol, where is your pestilence? Compassion is forever hidden from my eyes. (Sheol h7585)
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Though he is flourishing among his brothers, there will come an east wind, the Lord’s wind, coming up from the wilderness. His fountain will dry up, his spring will be parched. The wind will strip the treasury, all the precious things.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Samaria will bear her guilt, for she has rebelled against her God. They will fall by the sword, their children dashed to pieces, their pregnant women ripped open.

< Hosiya 13 >