< Hosiya 13 >
1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
When Ephraim spoke, there was trembling, he exalted himself in Israel; but when he became guilty through Baal, he died.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
And now they sin more and more, and have made them molten images of their silver, according to their own understanding, even idols, all of them the work of the craftsmen; of them they say: 'They that sacrifice men kiss calves.'
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Therefore they shall be as the morning cloud, and as the dew that early passeth away, as the chaff that is driven with the wind out of the threshing-floor, and as the smoke out of the window.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
Yet I am the LORD thy God from the land of Egypt; and thou knowest no God but Me, and beside Me there is no saviour.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
I did know thee in the wilderness, in the land of great drought.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
When they were fed, they became full, they were filled, and their heart was exalted; therefore have they forgotten Me.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
Therefore am I become unto them as a lion; as a leopard will I watch by the way;
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
I will meet them as a bear that is bereaved of her whelps, and will rend the enclosure of their heart; and there will I devour them like a lioness; the wild beast shall tear them.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
It is thy destruction, O Israel, that thou art against Me, against thy help.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Ho, now, thy king, that he may save thee in all thy cities! and thy judges, of whom thou saidst: 'Give me a king and princes!'
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
I give thee a king in Mine anger, and take him away in My wrath.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
The iniquity of Ephraim is bound up; his sin is laid up in store.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
The throes of a travailing woman shall come upon him; he is an unwise son; for it is time he should not tarry in the place of the breaking forth of children.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
Shall I ransom them from the power of the nether-world? Shall I redeem them from death? Ho, thy plagues, O death! Ho, thy destruction, O nether-world! Repentance be hid from Mine eyes! (Sheol )
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
For though he be fruitful among the reed-plants, an east wind shall come, the wind of the LORD coming up from the wilderness, and his spring shall become dry, and his fountain shall be dried up; he shall spoil the treasure of all precious vessels.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Samaria shall bear her guilt, for she hath rebelled against her God; they shall fall by the sword; their infants shall be dashed in pieces, and their women with child shall be ripped up.