< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
According to the word of Ephraim he adopted ordinances for himself in Israel; and he established them for Baal, and died.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
And now they have sinned increasingly, and have made for themselves a molten image of their silver, according to the fashion of idols, the work of artificers accomplished for them: they say, Sacrifice men, for the calves have come to an end.
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Therefore shall they be as a morning cloud, and as the early dew that passes away, as chaff blown away from the threshing-floor, and as a vapor from tears.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
But I am the Lord thy God that establishes the heaven, and creates the earth, whose hands have framed the whole host of heaven: but I shewed them not to thee that thou shouldest go after them: and I brought thee up out of the land of Egypt, and thou shalt know no God but me; and there is no Saviour beside me.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
I tended thee as a shepherd in the wilderness, in an uninhabited land.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
According to their pastures, so they were completely filled; and their hearts were exalted; therefore they forgot me.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
And I will be to them as a panther, and as a leopard.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
I will meet them by the way of the Assyrians, as a she-bear excited, and I will rend the caul of their heart, and the lions' whelps of the thicket shall devour them there; the wild beasts of the field shall rend them in pieces.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
O Israel, who will aid [thee] in thy destruction?
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Where is this thy king? let him even save thee in all thy cities: let him judge thee, of whom thou saidst, Give me a king and a prince.
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
And I gave thee a king in mine anger, and kept [him] back in my wrath.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
Ephraim [has framed] a conspiracy of unrighteousness, his sin is hidden.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
Pains as of a woman in travail shall come upon him: he is thy wise son, because he shall not stay in the destruction of [thy] children.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
I will deliver [them] out of the power of Hades, and will redeem them from death: where is thy penalty, O death? O Hades, where is thy sting? comfort is hidden from mine eyes. (Sheol h7585)
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Forasmuch as he will cause a division among [his] brethren, the Lord shall bring upon him an east wind from the desert, and shall dry up his veins [and] quite drain his fountains: he shall dry up his land, and [spoil] all his precious vessels.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Samaria shall be utterly destroyed: for she has resisted her God; they shall fall by the sword, and their sucklings shall be dashed against the ground, and their women with child ripped up.

< Hosiya 13 >