< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
Naar Efraim talte, var der Skræk, han ophøjede sig i Israel; men han blev skyldig ved Baal og døde.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
Og nu blive de ved at synde og gøre sig støbte Billeder af deres Sølv, Afguder efter deres Forstand, alt sammen Kunstneres Værk; om dem sige de, nemlig de Mennesker, som ofre, at de skulle kysse Kalve.
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Derfor skulle de vorde som en Sky om Morgenen og som Duggen, der aarle gaar bort, som Avner, der vejres bort fra Tærskepladsen, og som Røg ud af et Vindue.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
Men jeg er Herren din Gud fra Ægyptens Land af, og en Gud uden mig kender du ikke, og en Frelser uden mig er der ikke.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
Jeg, jeg kendte dig i Ørken, i det tørre Land.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
Som de kom paa Græsgang, bleve de mætte, de bleve mætte, og deres Hjerte ophøjede sig; derfor glemte de mig.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
Og jeg blev dem som en Løve, som en Parder lurer jeg paa Vejen.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Jeg vil anfalde dem som en Bjørn, der er berøvet sine Unger, og vil sønderrive deres Hjertes Lukke, og jeg vil fortære dem der som en Løvinde, Markens Dyr skulle sønderslide dem.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
Det var din Fordærvelse, Israel! at du var imod mig, imod din Hjælp.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Hvor er nu din Konge, at han kan frelse dig i alle dine Stæder? og dine Dommere, om hvilke du sagde: Giv mig Konge og Fyrster?
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
Jeg giver dig en Konge i min Vrede og tager ham bort i min Harme.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
Efraims Misgerning er sammenbunden, hans Synd er gemt.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
Smerter skulle komme paa ham som paa Kvinden, der føder; han er ikke en viis Søn, thi han burde ikke en Tid blive staaende i Fødselens Gennembrud.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
Af Dødsrigets Vold vil jeg forløse dem, fra Døden vil jeg genløse dem; Død! hvor er din Pest? Dødsrige! hvor er din ødelæggende Magt? Fortrydelse er skjult for mine Øjne. (Sheol h7585)
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Thi han skal bære Frugt iblandt Brødre; dog skal der komme et Østenvejr, et Herrens Vejr, som drager op fra Ørken, og hans Væld skal udtørres og hans Kilde blive tør; det skal røve Skatten af alle kostelige Kar.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Samaria skal bøde, thi den har været genstridig imod Gud; de skulle falde ved Sværdet, deres spæde Børn skulle knuses og deres frugtsommelige Kvinder sønderrives.

< Hosiya 13 >