< Hosiya 13 >
1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
Když mluvíval Efraim, býval strach; vznešený byl v Izraeli, ale prohřešiv při Bálovi, tožť umřel.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
A i nyní ještě předce hřeší. Nebo dělají sobě a slévají z stříbra svého podlé rozumu svého strašidla, ješto všecko to není než dílo řemeslníků, o čemž říkají: Lidé, kteříž obětují, telata ať líbají.
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
Protož budou jako oblak ranní a jako rosa jitřní, kteráž odchází, jako plevy vichřicí zachvácené z humna, a jako dým z komínu,
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
Ješto já jsem Hospodin Bůh tvůj od vyjití z země Egyptské, a Boha kromě mne nepoznal jsi, aniž jest jiný vysvoboditel kromě mne.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
Jáť jsem tě poznal na poušti v zemi velmi vyprahlé.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
Dobré pastvy měvše, nasyceni jsou, ale když se nasytili, pozdvihlo se srdce jejich, protož zapomenuli na mne.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
Pročež budu jim jako lítý lev, jako pardus vedlé cesty číhati budu.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Potkám se s nimi jako nedvěd osiřelý, a roztrhám všecko srdce jejich, a sežeru je tam jako lev, jako zvěř divoká roztrhující je.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
Z tebeť jest zhouba tvá, ó Izraeli, ješto ve mně všecka pomoc tvá.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Kdež jest král tvůj? Kdež jest? Nechť tě zachová ve všech městech tvých. Aneb soudcové tvoji, o nichž jsi řekl: Dej mi krále a knížata?
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
Dal jsem tobě krále v hněvě svém, a odjal jsem v prchlivosti své.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
Svázánať jest nepravost Efraimova, schován jest hřích jeho.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
Bolesti rodičky přijdou na něj; jest syn nemoudrý, sic jinak nezůstával by tak dlouho v životě matky.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
Z ruky hrobu vyplatím je, od smrti vykoupím je; budu zhoubcím tvým, ó smrti, budu zkažením tvým, ó hrobe, želení skryto bude od očí mých. (Sheol )
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Nebo on mezi bratřími ovoce ponese, ač prv přijde vítr východní, vítr Hospodinův od pouště vstupující, a vysuší studnice jeho, osuší i vrchoviště jeho; onenno rozchvátá poklad všech nejdražších klénotů.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Zpuštěna bude Samaří, proto že se protivila Bohu svému; od meče padnou, dítky jejich zrozrážíny budou, a těhotné ženy jejich zroztínány.