< Hosiya 12 >

1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Efraín trata de guiar al viento, yendo tras el viento del este todo el día. Sus mentiras y su violencia siguen en aumento. Hicieron un tratado con Asiria, y envían el aceite de oliva a Egipto.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
El Señor tiene además una acusación en contra de Judá, y castigará a Jacob por las acciones del pueblo. Les pagará conforme a lo que han hecho.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
Incluso desde el vientre Jacob luchó con su hermano; y cuando se hizo hombre luchó con Dios.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Peleó con un ángel y ganó. Lloró y le rogó por una bendición. Jacob encontró a Dios en Betel, y allí habló con él,
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
el Señor Dios Todopoderoso, ¡el Señor es su gran nombre!
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Ustedes deben volver a su Dios. Actúen con amor y hagan lo recto, y siempre esperen en Dios.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
El mercader que sostiene en sus manos una balanza alterada ama la estafa.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Efraín dice: “Soy rico! ¡Me he enriquecido! He recibido mucho fruto de mi trabajo y nadie puede demostrar que soy culpable de ningún mal”.
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Pero yo soy el Señor tu Dios, que te saqué de la tierra de Egipto. Yo te hare vivir de nuevo en tiendas como lo haces en tiempos de fiesta.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
Yo hablé a través de los profetas. Yo mismo di muchas visiones y parábolas a través de los profetas.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Si Galaad es idólatra, sin duda se volverán nada. Sacrifican toros en Guilgal. Incluso sus altares son como pilas de rocas en los surcos del campo.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob huyó a la tierra de Harán; Israel trabajó allí para ganarse una esposa. Se ganó una esposa cuidando ovejas.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
A través de un profeta el Señor sacó a Israel de Egipto, y fueron cuidados por un profeta también.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Efraín ha hecho enojar al Señor, y el Señor los dejará sufrir las consecuencias de su derramamiento de sangre, y les pagará por su desprecio.

< Hosiya 12 >