< Hosiya 12 >
1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Efraím se apacienta de viento, y corre tras el viento del oriente, todo el día está aumentando las mentiras y los actos de violencia; hace pacto con Asiria, y a Egipto lleva aceite.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
También contra Judá se querellará Yahvé, y castigará a Jacob conforme a su conducta; según sus obras le retribuirá.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
En el seno materno suplantó a su hermano, y en su edad madura luchó con Dios.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Luchó con el ángel, y prevaleció; lloró y le pidió gracia. En Betel le halló, y allí habló con nosotros.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
Yahvé que es el Dios de los ejércitos; Yahvé es su Nombre.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
“Conviértete a tu Dios; guarda la misericordia y la justicia, y espera siempre en tu Dios”.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
Siendo mercader, que tiene en sus manos balanza falsa, se complace en engañar.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Dice Efraím: “Con todo, me he hecho rico, he adquirido riquezas; con todas mis ganancias no se hallará en mí culpa que sea pecado.”
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Yo soy Yahvé, tu Dios, desde la tierra de Egipto; Yo haré que habites otra vez en tiendas, como en días de la fiesta.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
Yo hablé a los profetas, haciéndoles ver muchas visiones; por medio de los profetas me he manifestado en parábolas.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Si Galaad es vanidad, también ellos son vanidad. En Gálgala sacrifican toros, y sus altares son como montones de piedras en los surcos del campo.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Huyó Jacob al país de Siria, por una mujer Israel se hizo siervo, y por una esposa apacentó (ovejas).
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Por mano de un profeta Yahvé sacó a Israel de Egipto, y lo salvó por medio de un profeta.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Efraím ha provocado a su Señor con amargos pecados; por lo cual hará caer sobre él la sangre derramada, y le dará la paga por sus ultrajes.