< Hosiya 12 >
1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraim se apascenta de vento, e segue o vento leste: todo o dia multiplica a mentira e a destruição; e fazem aliança com a Assyria, e o azeite se leva ao Egito.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
O Senhor também com Judá tem contenda, e fará visitação sobre Jacob segundo os seus caminhos; segundo as suas obras lhe recompensará.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
No ventre pegou do calcanhar de seu irmão, e pela sua força como príncipe se houve com Deus.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Como príncipe se houve com o anjo, e prevaleceu; chorou, e lhe suplicou: em bethel o achou, e ali falou conosco,
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
A saber, o Senhor, o Deus dos exércitos: o Senhor é o seu memorial.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Tu, pois, converte-te a teu Deus: guarda a beneficência e o juízo, e em teu Deus espera sempre.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
Na mão do mercador está uma balança enganosa; ama a opressão.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Ainda diz Ephraim: contudo eu estou enriquecido, e tenho adquirido para mim grandes bens: em todo o meu trabalho não acharão em mim iniquidade alguma que seja pecado.
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Mas eu sou o Senhor teu Deus desde a terra do Egito: eu ainda te farei habitar em tendas, como nos dias do ajuntamento.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
E falarei aos profetas, e multiplicarei a visão; e pelo ministério dos profetas proporei similes.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Porventura não é Gilead iniquidade? pura vaidade são: em Gilgal sacrificam bois: os seus altares como montões de pedras são nos regos dos campos.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob fugiu para o campo da Síria, e Israel serviu por sua mulher, e por sua mulher guardou o gado.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Mas o Senhor por um profeta fez subir a Israel do Egito, e por um profeta foi ele guardado.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Ephraim porém mui amargosamente o irou: portanto deixará ficar sobre ele o seu sangue, e o seu Senhor lhe recompensará o seu opróbrio.