< Hosiya 12 >

1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraïm se repaît de vent et poursuit un air brûlant; tout le jour il multiplie le mensonge et la dévastation; il a fait alliance avec les Assyriens et il portait de l’huile en Egypte.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
Voici donc venir le jugement du Seigneur avec Juda, et sa visite sur Jacob; il lui rendra selon ses voies et ses inventions.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
Dans le sein maternel il supplanta son frère; par sa force il lutta avec l’ange.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Et il prévalut contre l’ange et il fut fortifié; il pleura, et le pria: il le trouva à Béthel, et là le Seigneur nous parla.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
Et le Seigneur, le Dieu des armées, le Seigneur devint l’objet de son souvenir.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Et toi, Israël, à ton Dieu tu te convertiras; garde la miséricorde et le jugement, et espère en ton Dieu, toujours.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
Quant à Chanaan, dans sa main est une balance trompeuse; il a aimé l’oppression.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Et Ephraïm a dit: Cependant je suis devenu riche, j’ai trouvé une idole pour moi; aucun de mes travaux ne trouvera l’iniquité par laquelle j’ai péché.
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Et moi, je suis le Seigneur ton Dieu, depuis que je t’ai retiré de la terre d’Egypte; je te ferai encore demeurer dans des tabernacles comme aux jours de fête.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
Et j’ai parlé aux prophètes, et c’est moi qui ai multiplié les visions; et par le ministère des prophètes j’ai été assimilé aux hommes.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Si Galaad était une idole, c’est donc en vain qu’ils sacrifiaient aux bœufs de Galgal; car leurs autels sont comme des monceaux de pierre sur les sillons des champs.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob a fui dans la contrée de Syrie, et Israël a servi pour une femme, et pour une autre femme il a servi.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Par un prophète, le Seigneur a tiré Israël de l’Egypte, et par un prophète il a été conservé.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Par ses plaintes amères, Ephraïm m’a provoqué au courroux; et son sang retombera sur lui, et son opprobre, le Seigneur le lui rendra.

< Hosiya 12 >