< Hosiya 12 >
1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Éphraïm se repaît de vent, et poursuit le vent d'orient. Chaque jour il multiplie le mensonge et la violence; il traite alliance avec Assur, et on porte l'huile en Égypte.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
L'Éternel est aussi en procès avec Juda, et il punira Jacob à cause de ses voies; il lui rendra selon ses œuvres.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
Dès le sein maternel il supplanta son frère, et dans sa force il lutta avec Dieu.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Il lutta avec l'ange, et il fut le plus fort; il pleura, et lui demanda grâce. A Béthel il le trouva, et c'est là que Dieu nous a parlé.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
L'Éternel est le Dieu des armées; son nom est l'Éternel.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Toi donc, reviens à ton Dieu; garde la miséricorde et la justice; et espère continuellement en ton Dieu.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
Éphraïm est un marchand, qui a dans sa main des balances fausses; il aime à frauder.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Et Éphraïm dit: “Oui, je suis devenu riche; je me suis acquis des richesses. Dans tout mon travail on ne trouvera aucune injustice, rien qui soit un péché. “
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Et moi, je suis l'Éternel ton Dieu dès le pays d'Égypte. Je te ferai encore habiter sous des tentes, comme aux jours de fête.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
J'ai parlé aux prophètes, et j'ai multiplié les visions, et par le moyen des prophètes j'ai proposé des similitudes.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Si Galaad n'est qu'iniquité, certainement ils seront réduits à néant. Ils ont sacrifié des bœufs à Guilgal; aussi leurs autels seront comme des monceaux de pierres sur les sillons des champs.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob s'enfuit au pays de Syrie, et Israël servit pour une femme, et pour une femme il garda les troupeaux.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Et par un prophète l'Éternel fit monter Israël hors d'Égypte; et par un prophète Israël fut gardé.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Éphraïm a provoqué une amère indignation; aussi son Seigneur laissera-t-il peser sur lui le sang qu'il a répandu, et lui rendra ses mépris.