< Hosiya 12 >

1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraïm se repaît de vent, et va après le vent d'Orient; il multiplie tous les jours ses mensonges et le dégât, et ils traitent alliance avec l'Assyrie, et l'on porte des huiles de senteur en Egypte.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
L'Eternel a aussi un procès avec Juda, et il visitera Jacob selon son train, il lui rendra selon ses œuvres.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
Dès le ventre il supplanta son frère, puis par sa force il fut vainqueur [en luttant] avec Dieu.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Il fut vainqueur [en luttant] avec l'Ange, et fut le plus fort; il pleura, et lui demanda grâce; il le trouva à Béthel, et là [Dieu] parla avec nous.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
Or l'Eternel est le Dieu des armées; son mémorial, c'est L'[Eternel].
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Toi donc retourne-toi à ton Dieu; garde la miséricorde et le jugement, et aie continuellement espérance en ton Dieu.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
[Ephraïm] est un marchand; il y a en sa main des balances trompeuses; il aime à faire des extorsions.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Et Ephraïm a dit: Quoi qu'il en soit, je suis devenu riche; je me suis acquis des richesses; pas un de mes travaux ne feront trouver en moi une iniquité qui soit un péché.
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Et moi je suis l'Eternel ton Dieu dès le pays d'Egypte; je te ferai encore habiter dans des tentes, comme aux jours de fête solennelle.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
Je parlerai par les Prophètes, et multiplierai les visions, et je proposerai des similitudes par le moyen des Prophètes.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Certainement Galaad n'est qu'iniquité, certainement ils ne sont que vanité; ils ont sacrifié des bœufs en Guilgal; même leurs autels sont comme des monceaux sur les sillons des champs.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Or Jacob s'enfuit au pays de Syrie, et Israël servit pour une femme, et pour une femme il garda le bétail.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Puis l'Eternel fit remonter Israël hors d'Egypte par le Prophète, et il fut gardé par le Prophète.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
[Mais] Ephraïm a provoqué [Dieu] à une amère indignation, c'est pourquoi on répandra son sang sur lui, et son Seigneur lui rendra son opprobre.

< Hosiya 12 >