< Hosiya 12 >

1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraim feeds on the wind and follows after the east wind. He continually multiplies lies and violence. They make a covenant with Assyria and carry olive oil to Egypt.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
Yahweh also has a lawsuit against Judah and will punish Jacob for what he has done; he will repay him for his deeds.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
In the womb Jacob grasped his brother by the heel, and in his manhood he struggled with God.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
He struggled with the angel and won. He wept and begged for his favor. He met God at Bethel; there God spoke with him.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
This is Yahweh, the God of hosts; “Yahweh” is his name to be called on.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
So turn to your God. Keep covenantal faithfulness and justice, and wait continually for your God.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
The merchants have false scales in their hands; they love to defraud.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Ephraim said, “I have certainly become very rich; I have found wealth for myself. In all my work they will not find any iniquity in me, anything that would be sin.”
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
“I am Yahweh your God from the land of Egypt. I will again make you live in tents, as in the days of the appointed festival.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
I spoke to the prophets, and I gave them many visions for you. By the hand of the prophets I gave parables.”
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
If there is wickedness in Gilead, surely the people are worthless. In Gilgal they sacrifice bulls; their altars will be like heaps of stone in the furrows of the fields.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob fled to the land of Aram; Israel worked in order to get a wife; and he kept flocks of sheep to get a wife.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Yahweh brought Israel out of Egypt by a prophet, and by a prophet he took care of them.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Ephraim has bitterly angered Yahweh. So his Lord will leave his blood on him and will turn back on him his disgrace.

< Hosiya 12 >