< Hosiya 12 >

1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
[The leaders of] Israel are constantly wavering [about seeking help from other countries]. [Seeking their help is as useless as] [MET] chasing the wind. They pile up their lies and violent acts. [First, ] they make a treaty with Assyria, and [then they] send olive oil to [the rulers of] Egypt [to seek their help].
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
Yahweh [says that he] will bring accusations against [the leaders of] Judah, and that he will punish [the descendants of] Jacob for what they have done.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
[When Jacob was] in his mother’s womb, he grabbed his brother [Esau’s] heel [because he wanted to be born first]. When Jacob grew up, he wrestled with God.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
He struggled with [the one who had appeared to him in the form of] an angel, and Jacob defeated him, but [then] he cried and asked the angel to bless him. [Later], God came to Jacob at Bethel and talked with him there.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
[That was] the Commander of the armies of angels whose name is Yahweh [who talked with him]!
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
But you [people of Israel] must return to your God! You must faithfully love [him], and you must do what is fair/just and always depend on him.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
The merchants [among you] use scales that do not weigh correctly; they love/like to cheat people.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
[The people of] Israel boast, saying “We are [very] rich [DOU]; and we got all that money by our own efforts, and without committing any sin.”
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
“I am Yahweh your God, [the one who brought your ancestors] out of Egypt. [And some day] I will force you to live in tents again [like your ancestors did] when [they celebrated] the Festival [of Living in Temporary Shelters].
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
[Many times] I spoke to the prophets, and I gave them many visions, and I gave them parables to tell [to the people].”
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
[The people of] Gilead [city] are [RHQ] extremely wicked; they are worthless. The people sacrifice bulls in Gilgal [city], but their altars will [soon] become like [SIM] piles of stone [at the edge of] a plowed field.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
[Your ancestor] Jacob fled [from his brother Esau] and went to northwest Mesopotamia. He worked [for his uncle Laban for many years] to get a wife; he took care of [his uncle’s] sheep [to pay] for her.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
[Many years later, ] Yahweh enabled a prophet to bring the [ancestors of you] people of Israel here from Egypt; that prophet, [Moses], took care of them.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
[But now the people of] Israel have caused [Yahweh] to become very angry; Yahweh says that they deserve to die because they caused [many others] to die [MTY]; he will pay them back for the sins that they have committed against him and for insulting him.

< Hosiya 12 >