< Hosiya 12 >

1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraim feedeth on wind, and followeth after the east wind; Every day he multiplieth falsehood and violence; They make a league with Assyria, And oil is carried into Egypt.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
Therefore Jehovah hath a controversy with Judah. And he will punish Jacob for his ways, And requite him according to his doings.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
In the womb he took his brother by the heel, And in his strength he contended with God;
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Yea, he contended with the angel, and prevailed; He wept, and made supplication to him. At Bethel he found him, And there he spake with us.
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
And Jehovah, the God of hosts, Jehovah is his name.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Therefore turn thou to thy God; Observe mercy and justice, And hope in thy God always!
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
He is a Canaanite; in his hands are the balances of deceit; He loveth to oppress.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Yet Ephraim saith, Lo, I have become rich; I have found myself substance; In all my earnings can be found no transgression in which there is guilt.
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
Yet I, Jehovah, have been thy God from the land of Egypt; I will again cause thee to dwell in tents, as in the days of the solemn feast.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
I have also spoken to the prophets, And I have given many visions, And by the prophets I have used similitudes.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Behold, Gilead is full of iniquity; Surely they have become corrupt; In Gilgal they sacrifice oxen, And their altars are like the heaps in the furrows of the field.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob fled into the country of Syria, And Israel served for a wife, And for a wife he kept sheep.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
By a prophet Jehovah brought up Israel out of Egypt, And by a prophet was he preserved.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Ephraim hath provoked his Lord most bitterly; Therefore will he leave his blood upon him, And recompense to him his reproach.

< Hosiya 12 >