< Hosiya 12 >
1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraim feeds on wind, and follows after the east wind: he daily increases lies and desolation; and they do make a covenant with the Assyrians, and oil is carried into Egypt.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
The LORD has also a controversy with Judah, and will punish Jacob according to his ways; according to his doings will he recompense him.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
He took his brother by the heel in the womb, and by his strength he had power with God:
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
Yes, he had power over the angel, and prevailed: he wept, and made supplication to him: he found him in Bethel, and there he spoke with us;
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
Even the LORD God of hosts; the LORD is his memorial.
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Therefore turn you to your God: keep mercy and judgment and wait on your God continually.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
He is a merchant, the balances of deceit are in his hand: he loves to oppress.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
And Ephraim said, Yet I am become rich, I have found me out substance: in all my labors they shall find none iniquity in me that were sin.
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
And I that am the LORD your God from the land of Egypt will yet make you to dwell in tabernacles, as in the days of the solemn feast.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
I have also spoken by the prophets, and I have multiplied visions, and used similitudes, by the ministry of the prophets.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
Is there iniquity in Gilead? surely they are vanity: they sacrifice bullocks in Gilgal; yes, their altars are as heaps in the furrows of the fields.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
And Jacob fled into the country of Syria, and Israel served for a wife, and for a wife he kept sheep.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
And by a prophet the LORD brought Israel out of Egypt, and by a prophet was he preserved.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Ephraim provoked him to anger most bitterly: therefore shall he leave his blood on him, and his reproach shall his LORD return to him.