< Hosiya 12 >
1 Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
Ephraim tries to herd the wind, chasing after the east wind all day long. Their lies and violence keep on increasing. They make a treaty with Assyria, and send olive oil to Egypt.
2 Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
The Lord also has an accusation against Judah, and will punish Jacob for the way the people act; he will repay them for what they have done.
3 A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
Even in the womb he fought with his brother; when he became a man he fought with God.
4 Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
He fought with the angel, and he won. He wept, and begged him for a blessing. Jacob found God at Bethel, and spoke with him there—
5 Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
the Lord God Almighty, the Lord is his memorable name!
6 Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
You must return to your God. Act lovingly and do what is right, and always wait for your God.
7 Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
A merchant who holds in his hands dishonest scales loves to swindle.
8 Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
Ephraim says, “I'm rich! I've made myself wealthy! I've made so much from my work, and nobody can prove me guilty of doing wrong.”
9 “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
But I am the Lord your God who brought you out of the land of Egypt. I will make you live again in tents like you do at the time of that particular festival.
10 Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
I spoke through the prophets. I myself gave many visions and parables through the prophets.
11 Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
If Gilead is idolatrous, they will surely come to nothing. In Gilgal they sacrifice bulls. Even their altars are like heaps of rocks in the furrows of the field.
12 Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
Jacob fled to the land of Aram; Israel worked there to gain a wife, earning a wife by looking after sheep.
13 Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
Through a prophet the Lord brought Israel up from Egypt, and by a prophet they were cared for.
14 Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.
Ephraim has really upset the Lord, and the Lord will let them have the consequences of their bloodshed and pay them back for their contempt.