< Hosiya 11 >
1 “Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
Як Ізраїль був хлопцем, Я його покохав, і з Єгипту покликав Я сина Свого́.
2 Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
Як часто їх кликав, так вони йшли від Мене, — прино́сили жертви Ваа́лам, і кадили бовва́нам.
3 Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
Я ж Єфрема ходити навчав, Я їх брав на раме́на Свої, та не знали вони, що Я їх лікува́в.
4 Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
Я тягнув їх шнурка́ми, що лю́дям лицю́ють, шнурка́ми любови, і був Я для них немов ті, що здіймають ярмо́ з-над їхньої шиї, і Я їх годував.
5 “Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
До кра́ю єгипетського він не ве́рнеться, та Ашшур — він буде для нього царем, бо вони не хотіли верну́тись до Мене.
6 Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
А міста́ми його ґрасува́тиме меч, і за́суви його повила́млює він та й пожере́ їх за за́думи їхні.
7 Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
А наро́д Мій схильни́й відпада́ти від Мене, і хоч кличуть його догори, він не підійма́ється ра́зом.
8 “Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
Як тебе Я, Єфреме, відда́м, як ви́дам тебе́, о Ізраїлю? Як тебе Я віддам, як Адму, учиню тебе, мов Цевоїм? У Мені переверну́лося серце Моє, розпали́лася ра́зом і жа́лість Моя!
9 Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
Не вчиню́ жару гніву Свого, більше ни́щити Єфрема не бу́ду, бо Бог Я, а не люди́на, серед тебе — Святий, і не прийду́ в люті гніву.
10 Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
За Господом пі́дуть вони, а Він заричи́ть, немов лев, і Він заричи́ть, і від за́ходу при́йдуть в тремті́нні сини́.
11 Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
Вони при́йдуть в тремті́нні, як птах із Єгипту, і як голуб із кра́ю Ашшу́ра, і Я посаджу́ їх по їхніх дома́х, говорить Госпо́дь.
12 Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.
Єфре́м оточи́в Мене лжею, лука́вством — Ізраїлів дім, а Юда держа́вся ще з Богом і з святими був вірний.