< Hosiya 11 >

1 “Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
Da Israel var ung, hadde jeg ham kjær, og fra Egypten kalte jeg min sønn.
2 Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
Jo mere de kalte på dem, dess mere gikk de bort fra dem; de ofrer til Ba'alene og brenner røkelse for de utskårne billeder.
3 Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
Og det var da jeg som lærte Efra'im å gå og tok dem på mine armer; men de skjønte ikke at jeg lægte dem.
4 Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
Med menneskebånd drog jeg dem, med kjærlighets rep, og jeg var for dem som de som løfter op åket over kjevene, og jeg gav ham føde.
5 “Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
Han skal ikke vende tilbake til Egyptens land, men Assur skal være hans konge; for de vilde ikke vende om.
6 Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
Sverdet skal fare om i hans byer og tilintetgjøre hans bommer og ete om sig - for deres onde råds skyld;
7 Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
for mitt folk henger fast ved sitt frafall fra mig, og kaller nogen dem til det høie, er det ingen av dem som løfter sitt øie opad.
8 “Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
Hvorledes skal jeg kunne gi dig op, Efra'im, gi dig til pris, Israel? Hvorledes skal jeg kunne gi dig op som Adma, gjøre med dig som med Sebo'im? Mitt hjerte vender sig i mig, all min medynk våkner.
9 Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
Jeg vil ikke fullbyrde min brennende vrede, jeg vil ikke atter ødelegge Efra'im; for jeg er Gud og ikke et menneske, den Hellige i din midte; jeg kommer ikke med glødende harme.
10 Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
De skal følge Herren; han skal brøle som en løve; ja, han skal brøle, og bevende skal hans barn komme fra havet;
11 Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
bevende skal de komme som en fugl fra Egypten, som en due fra Assurs land, og jeg vil la dem bo i sine hus, sier Herren.
12 Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.
Efra'im har omringet mig med løgn, og Israels hus med svik; og Juda er ennu gjenstridig mot Gud, mot den trofaste Hellige.

< Hosiya 11 >