< Hosiya 11 >
1 “Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
Quand Israël était jeune enfant, je l'ai aimé, et j'ai appelé mon fils hors d'Egypte.
2 Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
Lorsqu'on les appelait, ils s'en sont allés de devant ceux qui les appelaient; ils ont sacrifié aux Bahalins, et ont fait des encensements aux images taillées.
3 Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
Et j'ai appris à Ephraïm à marcher; on l'a porté sur les bras, et ils n'ont point connu que je les avais guéris.
4 Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
Je les ai tirés avec des cordeaux d'humanité, et avec des liens d'amitié; et je leur ai été comme ceux qui enlèveraient le joug de dessus leur cou, et j'ai fait approcher de lui la viande.
5 “Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
Il ne retournera point au pays d'Egypte; mais le Roi d'Assyrie sera son Roi, parce qu'ils n'ont point voulu se convertir [à moi].
6 Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
L'épée s'arrêtera dans ses villes, et consumera ses forces, et les dévorera, à cause de leurs conseils.
7 Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
Et mon peuple pend attaché à sa rébellion contre moi; et on le rappelle au Souverain, mais pas un d'eux ne l'exalte.
8 “Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
Comment te mettrais-je, Ephraïm? [Comment] te livrerais-je, Israël? comment te mettrais-je comme j'ai mis Adama, et te ferais-je tel que Tséboïm? Mon cœur est agité dans moi, mes compassions se sont toutes ensemble échauffées.
9 Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
Je n'exécuterai point l'ardeur de ma colère, je ne retournerai point à détruire Ephraïm; car je suis le [Dieu] Fort, et non pas un homme; je suis le Saint au milieu de toi, et je n'entrerai point dans la ville.
10 Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
Ils marcheront après l'Eternel; il rugira comme un lion; et quand il rugira, les enfants accourront de l'Occident en hâte.
11 Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
Ils accourront en hâte hors d'Egypte, comme des oiseaux; et hors du pays d'Assyrie, comme des pigeons, et je les ferai habiter dans leurs maisons, dit l'Eternel.
12 Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.
Ephraïm m'a abordé avec des mensonges, et la maison d'Israël avec des tromperies, lorsque Juda dominait encore avec le [Dieu] Fort, et [qu'il était] fidèle avec les Saints.