< Hosiya 11 >
1 “Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
“When Israel was a young man I loved him, and I called my son out of Egypt.
2 Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
The more they were called, the more they went away from me. They sacrificed to the Baals and burned incense to idols.
3 Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
Yet it was I who taught Ephraim to walk. It was I who lifted them up by their arms, but they did not know that I cared for them.
4 Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
I led them with cords of humanity, with bands of love. I was to them like someone who eased the yoke on their jaws, and I bent down to them and fed them.
5 “Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
Will they not return to the land of Egypt? Will Assyria not rule over them because they refuse to return to me?
6 Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
The sword will fall on their cities and destroy the bars of their gates; it will destroy them because of their own plans.
7 Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
My people are determined to turn away from me. Though they call to the Most High, no one will help them.
8 “Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
How can I give you up, Ephraim? How can I hand you over, Israel? How can I make you like Admah? How can I make you like Zeboyim? My heart has changed within me; all my compassions have been stirred up.
9 Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
I will not execute my fierce anger; I will not again destroy Ephraim. For I am God and not a man; I am the Holy One among you, and I will not come in wrath.
10 Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
They will follow Yahweh; and he will roar like a lion. When he roars, his children will come trembling from the west.
11 Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
They will come trembling like a bird from Egypt, like a dove from the land of Assyria. I will make them live in their homes—this is the declaration of Yahweh.
12 Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.
Ephraim surrounds me with falsehood, and the house of Israel with deceit. But Judah is still going about with me, God, and is faithful to me, the Holy One.”