< Hosiya 10 >

1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israel es una vid exuberante que produce su fruto. Según la abundancia de sus frutos ha multiplicado sus altares. A medida que su tierra ha prosperado, han adornado sus piedras sagradas.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Su corazón está dividido. Ahora serán declarados culpables. Él demolerá sus altares. Destruirá sus piedras sagradas.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Seguramente ahora dirán: “No tenemos rey, porque no tememos a Yahvé; y el rey, ¿qué puede hacer por nosotros?”
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Hacen promesas, jurando en falso al hacer pactos. Por eso, el juicio brota como maleza venenosa en los surcos del campo.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
Los habitantes de Samaria estarán aterrorizados por los becerros de Bet Aven, porque su pueblo se lamentará por él, junto con sus sacerdotes que se regocijaron por ello, para su gloria, porque se ha apartado de ella.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
También será llevada a Asiria como regalo para un gran rey. Efraín recibirá la vergüenza, e Israel se avergonzará de su propio consejo.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samaria y su rey se alejan flotando como una ramita en el agua.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
Los lugares altos también de Aven, el pecado de Israel, serán destruidos. El espino y el cardo subirán a sus altares. Dirán a las montañas: “¡Cúbrenos!” y a las colinas: “¡Caigan sobre nosotros!”
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
“Israel, has pecado desde los días de Gabaa. Allí se quedaron. La batalla contra los hijos de la iniquidad no los alcanza en Gabaa.
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
Cuando sea mi deseo, los castigaré; y las naciones se reunirán contra ellos cuando están atados a sus dos transgresiones.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Efraín es una novilla amaestrada que le gusta trillar, así que pondré un yugo en su hermoso cuello. Pondré un jinete en Efraín. Judá arará. Jacob romperá sus terrones.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Sembrad para vosotros mismos en la justicia, cosechar según la bondad. Rompe tu barbecho, porque es hora de buscar a Yahvé, hasta que venga y haga llover justicia sobre ti.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
Has arado la maldad. Has cosechado iniquidad. Has comido el fruto de la mentira, porque confiaste en tu camino, en la multitud de tus valientes.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
Por eso se levantará un rugido de batalla entre tu pueblo, y todas sus fortalezas serán destruidas, como Shalman destruyó Beth Arbel en el día de la batalla. La madre fue despedazada con sus hijos.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
Así te hará Betel a causa de tu gran maldad. Al amanecer el rey de Israel será destruido.

< Hosiya 10 >