< Hosiya 10 >

1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
UIsrayeli ulivini elithululwayo, lizenzela izithelo; njengobunengi bezithelo zakhe wandisa amalathi akhe; ngobuhle belizwe lakhe wenza insika zakhe eziyizithombe zibe zinhle.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Iyehlukanisile inhliziyo yabo; khathesi bazakuba lecala; yona izabhidliza amalathi abo, ichithe insika zabo eziyizithombe.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Ngoba khathesi bazakuthi: Kasilankosi; ngoba kasimesabanga uJehova; pho, inkosi izakwenzani kithi?
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Bakhulume amazwi, befunga amanga besenza isivumelwano; ngakho isahlulelo sizahluma njengokhula oluyitshefu emifolweni yensimu.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
Abahlali beSamariya bazakwesaba ngenxa yethole leBeti-Aveni; ngoba abantu bayo bazalililela, labapristi balo ababethokoza ngalo, ngodumo lwalo, ngoba lusukile kulo.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
Yebo, lizathwalelwa eAsiriya, libe yisipho enkosini uJarebhi. UEfrayimi uzakuba lenhloni, loIsrayeli ayangeke ngenxa yeseluleko sakhe.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
ISamariya iqunyiwe, lenkosi yayo injengebazelo ebusweni bamanzi.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
Lendawo eziphakemeyo zeAveni, isono sikaIsrayeli, kuzachithwa; ameva lokhula oluhlabayo kuzamila phezu kwamalathi abo. Njalo bazakuthi ezintabeni: Sisibekeleni; lemaqaqeni: Welani phezu kwethu.
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
Kusukela ensukwini zeGibeya wonile, Israyeli; lapho bema; impi eGibeya emelene labantwana bobubi kayibaficanga.
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
Kusesiloyisweni sami ukubajezisa; izizwe zizabuthana zimelene labo, lapho ngizababopha ngenxa yeziphambeko zabo ezimbili.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Njalo uEfrayimi ulithokazi elifundisiweyo, elithanda ukubhula, kodwa mina ngedlule phezu kwentamo yakhe yobuhle; ngigadise uEfrayimi, uJuda uzalima, uJakobe uzaziharela.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Zihlanyeleleni ekulungeni, livune emuseni; qhathani ingqatho yenu; ngoba sekuyisikhathi sokuyidinga iNkosi, ize ifike, inise ukulunga phezu kwenu.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
Lilime inkohlakalo, lavuna isiphambeko, lidle izithelo zamanga; ngoba lithembele endleleni yenu, ebunengini bamaqhawe enu.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
Ngalokho kuzakuba khona ukuxokozela phakathi kwabantu bakho, lenqaba zakho zonke zizachithwa, njengalokhu uShalimani wachitha iBeti-Aribeli ngosuku lwempi; unina wachotshozwa phezu kwabantwana.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
Izakwenza njalo iBhetheli kini, ngenxa yobubi bobubi bakho; emadabukakusa inkosi yakoIsrayeli izaqunywa lokuqunywa.

< Hosiya 10 >