< Hosiya 10 >

1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israël était une vigne couverte de feuilles, le fruit les égalait; selon l’abondance de son fruit elle a multiplié ses autels; suivant la fertilité de sa terre, elle a été féconde en simulacres.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Leur cœur s’est partagé, maintenant ils périront; lui-même brisera leurs simulacres, il renversera leurs autels.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Parce qu’alors ils diront: Nous n’avons pas de roi; car nous ne craignons pas le Seigneur; et le roi, que nous fera-t-il?
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Vous prononcez les paroles d’une vision inutile, et vous ferez une alliance; et le jugement du Seigneur germera comme l’herbe amère sur les sillons d’un champ.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
Les habitants de Samarie ont adoré les vaches de Bethaven; parce que le peuple a pleuré sur lui, et les gardiens de son temple se sont réjouis de sa gloire, parce qu’elle s’est éloignée de lui.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
Puisque lui-même a été porté en Assyrie, en présent à un roi vengeur; la confusion couvrira Ephraïm, et Israël sera confondu dans ses desseins.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samarie a fait disparaître son roi comme l’écume sur la surface de l’eau.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
Les hauteurs de l’idole, péché d’Israël, seront dévastées; la bardane et le chardon monteront sur leurs autels; et eux diront aux montagnes: Couvrez-nous; et aux collines: Tombez sur nous.
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
Depuis les jours de Gabaa, Israël a péché; là ils se sont arrêtés; ce ne sera pas une guerre comme à Gabaa contre des enfants d’iniquité, qui les atteindra.
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
Selon mon désir, je les châtierai; les peuples s’assembleront contre eux, lorsqu’ils seront châtiés pour leur double iniquité.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Ephraïm est une génisse qu’on a apprise à aimer le battage, et moi j’ai passé sur son beau cou; je monterai sur Ephraïm; Juda labourera et Jacob tracera par lui-même des sillons.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Semez pour vous dans la justice, et vous moissonnerez en proportion de votre miséricorde, mettez votre terre en novale; mais il sera temps de rechercher le Seigneur, lorsque sera venu celui qui vous enseignera la justice.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
Vous avez cultivé l’impiété, vous avez moissonné l’iniquité, vous avez mangé un fruit de mensonge, parce que tu t’es confié en tes voies, en la multitude de tes braves.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
Le tumulte s’élèvera parmi ton peuple, et toutes les fortifications seront dévastées, comme fut dévasté Salmana au jour du combat par la maison de celui qui jugea Baal, la mère ayant été écrasée sur les enfants,
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
Ainsi vous a fait Béthel, à cause de la malice de vos méchancetés.

< Hosiya 10 >