< Hosiya 10 >
1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israël était une vigne riche en sarments, abondante en fruits; mais plus ses grappes se sont multipliées, plus il a multiplié ses autels, et plus il a recueilli les biens de la terre, plus il a élevé de colonnes.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Ils ont partagé leur cœur, et maintenant ils périront; Dieu Lui-même renversera leurs autels, et leurs colonnes s'écrouleront.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Et alors ils diront: Nous n'avons point de roi, parce que nous n'avons pas craint le Seigneur; et un roi, que fera-t-il pour nous?
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Il dira de vaines paroles et des raisons mensongères; il fera une alliance perverse, et les jugements de Dieu abonderont comme l'herbe sauvage dans les champs.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
Ceux de Samarie habiteront auprès du veau de la maison de On, car son peuple a pleuré sur lui. Et autant ils avaient irrité le Seigneur, autant ils se réjouiront de Sa gloire, parce qu'Il S'était éloigné d'eux.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
Et, après l'avoir lié pour les Assyriens, ils l'ont offert en présent au roi Jarim. Et il recevra en sa demeure Éphraïm, et Israël en ses conseils sera confondu.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samarie a renversé son roi comme un fétu qu'emporte le courant de l'eau.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
Et les autels d'or, péchés d'Israël, seront détruits, et les ronces et les mauvaises herbes pousseront sur leurs autels. Et ils diront aux montagnes: Cachez-nous; et aux collines: Écroulez-vous sur nous.
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
Depuis qu'il y a des collines, Israël a péché, et c'est là qu'ils se sont arrêtés; mais la guerre que l'on fera aux fils de l'iniquité
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
ne se bornera pas à les surprendre sur une colline pour les châtier. Les peuples se réuniront contre eux, pour qu'ils soient punis de leur double péché.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Éphraïm est une génisse instruite à aimer la révolte; mais Moi Je tomberai sur son cou superbe; Je monterai sur Éphraïm, Je forcerai Juda au silence; Jacob prévaudra contre lui.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Semez pour vous-mêmes avec équité; recueillez les fruits de la vie; éclairez-vous de la lumière de la science, et cherchez le Seigneur jusqu'à ce que les fruits de la justice vous arrivent.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
Mais pourquoi gardez-vous le silence sur votre impiété et récoltez-vous des injustices? Tu as mangé le fruit du mensonge, parce que tu as mis ton espérance en tes péchés et dans la multitude de tes forces.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
Mais la perdition s'élèvera parmi ton peuple, et tous les remparts disparaîtront. Comme le prince Salaman partit de la maison de Jéroboam durant les jours de la guerre, et jeta à terre avec violence les mères sur les enfants.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
De même Je te traiterai, ô maison d'Israël, à la vue de tes injustices et de tes méchancetés. Ils sont tombés dès l'aurore: le roi d'Israël est tombé.