< Hosiya 10 >

1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israël est une vigne luxuriante, qui s’est chargée de fruit. Plus ses fruits étaient abondants, plus il a multiplié les autels; plus le pays était beau, plus belles ils ont fait les stèles.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Leur cœur est hypocrite: ils vont en porter la peine. Lui, il renversera leurs autels, il détruira leurs stèles.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Bientôt ils diront: « Nous n’avons plus de roi; parce que nous n’avons pas craint Yahweh; et le roi, que fera-t-il pour nous? »
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Ils diront des paroles, faisant de vains serments, concluant des alliances, et le jugement éclôt comme le pavot, dans les sillons des champs.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
Pour les génisses de Bethaven, les habitants de Samarie ont peur; car son peuple prend le deuil sur l’idole, et ses prêtres tremblent à son sujet, pour sa gloire qui a émigré loin de lui.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
Elle aussi, on la transportera en Assyrie, comme offrande au roi vengeur; la confusion saisira Ephraïm; Israël aura honte de ses desseins.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samarie est anéantie; son roi est comme un fétu sur la surface de l’eau.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
Ils seront détruits les hauts lieux d’Aven, péché d’Israël; l’épine et la ronce monteront sur leurs autels. Ils diront aux montagnes: « Couvrez-nous! » et aux collines: « Tombez sur nous! »
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
Depuis les jours de Gabaa tu as péché, Israël; ils persévèrent dans le crime; ne les atteindra-t-elle pas à Gabaa, la guerre déclarée aux fils d’iniquité?
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
Je les châtierai à mon gré, et les peuples seront rassemblés contre eux, lorsqu’on les liera à leurs deux péchés.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Ephraïm était une génisse bien dressée, qui prenait plaisir à fouler le blé. Et moi, j’ai fait passer le joug sur son beau cou; j’attellerai Ephraïm, Juda labourera, Jacob traînera la herse.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Faites vos semences selon la justice, moissonnez selon la miséricorde, défrichez-vous des terres nouvelles; il est temps de chercher Yahweh, jusqu’à ce qu’il vienne répandre sur vous la justice.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
Mais vous avez labouré la méchanceté, vous avez moissonné l’iniquité, vous avez mangé le fruit du mensonge. Tu t’es confié dans tes propres voies, dans le grand nombre de tes vaillants.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
Le tumulte s’élève parmi ton peuple, et toutes tes forteresses seront dévastées, comme Salman dévasta Beth-Arbel, au jour de la guerre où la mère fut écrasée sur ses enfants.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
Voilà ce que vous a fait Béthel, à cause de votre extrême méchanceté. Vienne l’aurore, et c’en est fait du roi d’Israël!

< Hosiya 10 >