< Hosiya 10 >
1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israël est une vigne luxuriante qui produit son fruit. Selon l'abondance de ses fruits, il a multiplié ses autels. Au fur et à mesure que leurs terres ont prospéré, ils ont orné leurs pierres sacrées.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Leur cœur est divisé. Maintenant, ils seront reconnus coupables. Il démolira leurs autels. Il détruira leurs pierres sacrées.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
Maintenant, ils diront: « Nous n'avons pas de roi, car nous ne craignons pas Yahvé; et le roi, que peut-il faire pour nous? »
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
Ils font des promesses, jurent faussement en concluant des pactes. C'est pourquoi le jugement pousse comme de l'herbe empoisonnée dans les sillons du champ.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
Les habitants de Samarie seront dans la terreur à cause des veaux de Beth Aven, car son peuple se lamentera sur elle, ainsi que ses prêtres qui s'en sont réjouis, pour sa gloire, car il s'en est éloigné.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
Elle sera aussi transportée en Assyrie pour être offerte à un grand roi. Ephraïm recevra la honte, et Israël aura honte de son propre conseil.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samarie et son roi s'envolent comme une brindille sur l'eau.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
Les hauts lieux de l'Aven, le péché d'Israël, seront détruits. L'épine et le chardon monteront sur leurs autels. Ils diront aux montagnes: « Couvrez-nous! » et aux collines: « Tombez sur nous! »
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
« Israël, tu as péché depuis le temps de Guibea. Ils sont restés là. La bataille contre les enfants de l'iniquité ne les atteint pas à Gibéa.
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
Quand je le voudrai, je les châtierai; et les nations s'assembleront contre eux quand ils sont liés à leurs deux transgressions.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Ephraïm est une génisse dressée qui aime battre, alors je mettrai un joug sur son beau cou. Je mettrai un cavalier sur Ephraïm. Juda va labourer. Jacob va briser ses mottes.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Semez pour vous-mêmes dans la justice, récolter selon la bonté. Défrichez votre terrain en friche, car il est temps de chercher Yahvé, jusqu'à ce qu'il vienne et fasse pleuvoir la justice sur vous.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
Vous avez labouré la méchanceté. Vous avez récolté l'iniquité. Vous avez mangé le fruit du mensonge, car tu as eu confiance dans ta voie, dans la multitude de tes guerriers.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
C'est pourquoi un cri de guerre s'élèvera parmi ton peuple, et toutes vos forteresses seront détruites, comme Shalman a détruit Beth Arbel au jour de la bataille. La mère a été mise en pièces avec ses enfants.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
C'est ainsi que Béthel te traitera, à cause de ta grande méchanceté. Au lever du jour, le roi d'Israël sera détruit.