< Hosiya 10 >
1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israel is a luxuriant vine that produces his fruit. As his fruit increased, the more altars he built. As his land produced more, he improved his pillars.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Their heart is deceitful; now they must bear their guilt. Yahweh will demolish their altars; he will destroy their pillars.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
For then they will say, “We have no king, for we did not fear Yahweh, and a king—what could he do for us?”
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
They speak empty words and make covenants by swearing falsely. So justice springs up like poisonous weeds in the furrows of a field.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
The inhabitants of Samaria will be afraid because of the calves of Beth Aven. Its people mourned over them, as did those idolatrous priests who had rejoiced over them and their splendor, but they are no longer there.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
They will be carried to Assyria as a present for the great king. Ephraim will be disgraced, and Israel will be ashamed of its idol.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samaria's king will be destroyed, like a chip of wood on the surface of the water.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
The high places of wickedness will be destroyed. This is the sin of Israel! Thorns and thistles will grow over their altars. The people will say to the mountains, “Cover us!” and to the hills, “Fall on us!”
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
“Israel, you have sinned since the days of Gibeah; there you have remained. Will not war overtake the sons of wrong in Gibeah?
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
When I desire it, I will discipline them. The nations will gather together against them and put them in bonds for their double iniquity.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Ephraim is a trained heifer that loves to thresh the grain, so I will put a yoke on her fair neck. I will put a yoke on Ephraim; Judah will plow; Jacob will pull the harrow by himself.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Sow righteousness for yourselves, and reap the fruit of covenant faithfulness. Break up your unplowed ground, for it is time to seek Yahweh, until he comes and rains righteousness on you.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
You have plowed wickedness; you reaped injustice. You have eaten the fruit of deception because you trusted in your plans and in your many soldiers.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
So a tumult of war will rise among your people, and all your fortified cities will be destroyed. It will be as Shalman destroyed Beth Arbel on a day of battle, when mothers were dashed to pieces with their children.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
So it will happen to you, Bethel, because of your great wickedness. At daybreak the king of Israel will be completely cut off.”