< Hosiya 10 >

1 Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
Israel a vine full of branches, the fruit is agreeable to it: according to the multitude of his fruit he hath multiplied altars, according to the plenty of his land he hath abounded with idols.
2 Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
Their heart is divided: now they shall perish: he shall break down their idols, he shall destroy their altars.
3 Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
For now they shall say: We have no king: because we fear not the Lord: and what shall a king do to us?
4 Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
You speak words of an unprofitable vision, and you shall make a covenant: and judgment shall spring up as bitterness in the furrows of the field.
5 Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
The inhabitants of Samaria have worshipped the king of Bethaven: for the people thereof have mourned over it, and the wardens of its temple that rejoiced over it in its glory because it is departed from it.
6 Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
For itself also is carried into Assyria, a present to the avenging king: shame shall fall upon Ephraim, and Israel shall be confounded in his own will.
7 Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
Samaria hath made her king to pass as froth upon the face of the water.
8 Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
And the high places of the idol, the sin of Israel shall be destroyed: the bur and the thistle shall grow up over their altars: and they shall say to the mountains: Cover us; and to the hills: Fall upon us.
9 “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
From the days of Gabaa, Israel hath sinned, there they stood: the battle in Gabaa against the children of iniquity shall not overtake them.
10 Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
According to my desire I will chastise them: and the nations shall be gathered together against them, when they shall be chastised for their two iniquities.
11 Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
Ephraim is a heifer taught to love to tread out corn, but I passed over upon the beauty of her neck: I will ride upon Ephraim, Juda shall plough, Jacob shall break the furrows for himself.
12 Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
Sow for yourselves in justice, and reap in the mouth of mercy, break up your fallow ground: but the time to seek the Lord is, when he shall come that shall teach you justice.
13 Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
You have ploughed wickedness, you have reaped iniquity, you have eaten the fruit of lying: because thou hast trusted in thy ways, in the multitude of thy strong ones.
14 hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
A tumult shall arise among thy people: and all thy fortresses shall be destroyed as Salmana was destroyed, by the house of him that judged Baal in the day of battle, the mother being dashed in pieces upon her children.
15 Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.
So hath Bethel done to you, because of the evil of your iniquities.

< Hosiya 10 >