< Hosiya 1 >

1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
[I am] Hosea, the son of Beeri. Yahweh gave me these messages [at various times] during the years that Uzziah, Jotham, Ahaz, and Hezekiah were the kings of Judah, and Jeroboam the son of Jehoash was the King of Israel.
2 Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
When Yahweh first [began to] give messages to me [to tell to the people of Israel], he said to me, “Go and marry a prostitute. But [some of] her children will be born as a result of her having sex with men to whom she is not married. That will illustrate how the people of Israel have turned away from me and worship (idols/other gods).”
3 Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
So I married Gomer, the daughter of Diblaim. She became pregnant and gave birth to my son.
4 Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
Yahweh said to me, “Give him the name Jezreel, [which means ‘God scatters’], because I will soon punish the descendants [MTY] of [King] Jehu [by scattering them], because he killed many of my people at Jezreel [town]. [Some day] I will end the kingdom of Israel,
5 A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
by destroying the power [MTY] of [the army of] Israel in Jezreel Valley.”
6 Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
[Later] Gomer became pregnant [again], and she gave birth to a daughter. Yahweh said to me “Give her the name Lo-ruhamah, [which means ‘not loved],’ because I will no longer [show that I] love the people [MET] of Israel, and I will not forgive them [for the sins that they have committed].
7 Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
But I will [show that I] love the people [MTY] of Judah [by saving them from their enemies]. However, it will not be by weapons and armies or horses and chariots that I will save them. Instead, it will be by [the power that I], Yahweh their God, [have].”
8 Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
After Gomer had (weaned/stopped breast-feeding) Lo-ruhamah, she became pregnant again, and she gave birth to another son.
9 Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
Yahweh said “Give him the name Lo-ammi, [which means 'not my people', ] because the people of Israel are no [longer my people], and I am not their God.
10 “Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
But [some day] the people of Israel will be [as numerous] as [SIM] the [grains of] sand on the seashore; no one will be able to count them. Now [I] am saying to them, ‘You are not my people,’ but then people will say to them, ‘[You are the] children of God who is all-powerful.’
11 Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.
[At that time], the people of Judah and the people of Israel will unite. They will appoint one leader for all of them, and they will return from the countries [to which they have been (exiled/forced to go)]. That will be a great time; Jezreel [also means ‘God plants’, and it will be as though God will plant them in this country again].”

< Hosiya 1 >