< Ibraniyawa 1 >

1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
En tiempos pasados la palabra de Dios vino a nuestros padres por medio de los profetas, en diferentes partes y de diferentes maneras;
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
Pero ahora, al final de estos días, nos ha llegado a través de su Hijo, a quien ha dado todas las cosas por herencia, y por medio de quien hizo el universo; (aiōn g165)
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
Quien, siendo el resplandor de su gloria, la verdadera imagen de su sustancia, apoyando todas las cosas por la palabra de su poder, habiéndose entregado a sí mismo como una ofrenda para libertad de nuestros pecados, se sentó a la diestra de Dios en el cielo;
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
Convertido en superior que los ángeles, y que por herencia obtuvo nombre más excelente que el de ellos.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
¿A cuál de los ángeles dijo Dios en algún momento, Tú eres mi Hijo, hoy te he engendrado? o, seré su padre, y él será mi hijo?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
Y nuevamente, cuando está enviando a su único Hijo al mundo, él dice: Dejen que todos los ángeles de Dios le den culto.
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
Y de los ángeles dice: El hace que sus ángeles, sean como vientos y sus siervos como llamas de fuego.
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
Mas del Hijo dice: Tu asiento de poder, oh Dios, por los siglos de los siglos; y la vara de tu reino es vara de justicia. (aiōn g165)
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Has sido un amante de la justicia y un enemigo del mal; y así Dios, tu Dios, ha puesto el aceite de alegría en tu cabeza más que en la cabeza de aquellos que están contigo.
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Tú, Señor, al principio pusiste la tierra sobre su base, y los cielos son obra de tus manos:
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
Ellos llegarán a su fin; pero eres para siempre; envejecerán como una túnica;
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
Ellos serán enrollados como un paño, como un manto, y serán cambiados; pero tú eres el mismo y tus años no tendrán fin.
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
Pero, ¿de cuál de los ángeles ha dicho en algún momento: Toma asiento a mi derecha hasta que ponga a todos los que están contra ti bajo tus pies?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
¿No son todos espíritus ayudadores, que son enviados como siervos a aquellos cuya herencia será la salvación?

< Ibraniyawa 1 >