< Ibraniyawa 1 >
1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
In many places and in many ways, in past times, God spoke to the fathers through the Prophets;
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
lastly, in these days, he has spoken to us through the Son, whom he appointed as the heir of all things, and through whom he made the world. (aiōn )
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
And since the Son is the brightness of his glory, and the figure of his substance, and is carrying all things by the Word of his virtue, thereby accomplishing a purging of sins, he sits at the right hand of Majesty on high.
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
And having been made so much better than the Angels, he has inherited a name so much greater than theirs.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
For to which of the Angels has he ever said: “You are my Son; today have I begotten you?” Or again: “I will be a Father to him, and he shall be a Son to me?”
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
And again, when he brings the only-begotten Son into the world, he says: “And let all the Angels of God adore him.”
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
And about the Angels, certainly, he says: “He makes his Angels spirits, and his ministers a flame of fire.”
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
But about the Son: “Your throne, O God, is forever and ever. The scepter of your kingdom is a scepter of equity. (aiōn )
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
You have loved justice, and you have hated iniquity. Because of this, God, your God, has anointed you with the oil of exultation, above your companions.”
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
And: “In the beginning, O Lord, you founded the earth. And the heavens are the work of your hands.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
These shall pass away, but you will remain. And all will grow old like a garment.
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
And you will change them like a cloak, and they shall be changed. Yet you are ever the same, and your years will not diminish.”
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
But to which of the Angels has he ever said: “Sit at my right hand, until I make your enemies your footstool?”
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Are they not all spirits of ministration, sent to minister for the sake of those who shall receive the inheritance of salvation?