< Ibraniyawa 8 >

1 Abin da muke magana a nan shi ne, muna da irin wannan babban firist, wanda ya zauna a hannun dama na kursiyin Maɗaukaki a sama,
Poglavitno pa pri tem, kar pravimo: višjega duhovnika imamo takega, kateri sedí na desnici prestola veličastva v nebesih;
2 wanda yake hidima a cikin wuri mai tsarki, tabanakul na gaskiya wanda Ubangiji ne ya kafa, ba mutum ba.
Oskrbnik svetišča in šatora pravega, katerega je postavil Gospod in ne človek.
3 Da yake dole kowane babban firist da aka naɗa yă miƙa baye-baye da hadayu, haka ma wannan ya bukaci yă kasance da abin da zai miƙa.
Kajti vsak višji duhovnik se postavlja, da prinaša darí in žrtve, zato je potreba, da ima tudi tá kaj, kar bi prinašal.
4 Da a ce yana a duniya ne, da bai zama firist ba, domin a nan akwai mutanen da doka ta naɗa don su miƙa baye-baye.
Ako bi namreč bil na zemlji, še duhovnik bi ne bil, ker so duhovniki, da dari darujejo po postavi,
5 Suna hidima a cikin tsattsarkan wuri wanda yake hoto da kuma siffar abin da yake cikin sama. Shi ya sa aka gargaɗi Musa sa’ad da yana dab da gina tabanakul cewa, “Ka lura fa, ka yi kome daidai bisa ga zānen da aka nuna maka a kan dutsen.”
Kateri služijo po podobi in senci stvarî nebeških, kakor je Mojzes ukaz prejel, ko je napravljal šator: "Glej", pravi namreč, "da narediš vse po zgledu pokazanem ti na gori.
6 Amma hidimar da Yesu ya karɓa tana da fifiko a kan tasu, kamar yadda alkawarin da shi ne yake matsakanci ya fi na dā fifiko nesa, an kuma kafa shi a kan alkawura mafi kyau.
Sedaj pa je dobil odličnejšo službo, za kolikor je tudi boljše zaveze srednik, katera je ustanovljena na boljših obljubah.
7 Gama da a ce alkawari na fari ba shi da wani laifi, da ba sai an sāke neman wani ba.
Ako bi bila namreč ona prva bila brez pogreška, ne bi se iskalo drugi mesto.
8 Amma Allah ya sami mutane da laifi ya ce, “Ina gaya muku lokaci yana zuwa, sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Kajti grajajoč jim pravi: "Glej, dnevi pridejo, govori Gospod, in s hišo Izraelovo in s hišo Judovo sklenem novo zavezo;
9 Ba zai zama kamar irin alkawarin da na yi da kakanni-kakanninsu sa’ad da na kama hannunsu don in fitar da su daga Masar ba, domin ba su yi aminci da alkawarina ba, sai na juya musu baya, in ji Ubangiji.
Ne po zavezi, katero sem storil z njih očeti, tisti dan, ko sem zgrabil njih roko, da bi jih izpeljal iz zemlje Egiptovske; ker oni niso ostali v zavezi moji, in jaz sem jih v nemar pustil, govori Gospod;
10 Wannan shi ne alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila, bayan lokacin nan, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu. Zan zama Allahnsu, su kuwa za su zama mutanena.
Ker to je zaveza, katero bodem sklenil s hišo Izraelovo, po tistih dnevih, govori Gospod: Postave svoje dam v njih misli, in v srca njih jih zapišem; in bodem jim za Boga, in oni mi bodejo za ljudstvo.
11 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa ba, balle mutum yă ce wa ɗan’uwansa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin dukansu za su san ni, daga ƙaraminsu zuwa babba.
In ne učé naj vsak svojega bližnjega, in vsak svojega brata, rekoč: Spoznavaj Gospoda; ker poznali me bodo vsi, od njih malega do njih velikega;
12 Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuma ƙara tuna da zunubansu ba.”
Ker milosten bodem njih krivicam, in njih grehov in pregreškov njih ne bodem se več spominjal."
13 Ta wurin kira wannan alkawari “sabo,” ya mai da na farin tsoho ke nan; abin da yake tsoho yana kuma daɗa tsufa, zai shuɗe nan ba da daɗewa ba.
Ker pravi: "Novo," ostaral je prvo; kar pa je ostarano in se stara, je skoraj minilo.

< Ibraniyawa 8 >