< Ibraniyawa 8 >

1 Abin da muke magana a nan shi ne, muna da irin wannan babban firist, wanda ya zauna a hannun dama na kursiyin Maɗaukaki a sama,
Voici maintenant, après tout ce que nous venons de dire, le point capital: Ce grand-prêtre que nous avons est tel qu'«il s'est assis à la droite!» du trône de la majesté divine, dans les cieux,
2 wanda yake hidima a cikin wuri mai tsarki, tabanakul na gaskiya wanda Ubangiji ne ya kafa, ba mutum ba.
comme ministre du sanctuaire et du vrai «tabernacle, dressé par le Seigneur» et non par un homme.
3 Da yake dole kowane babban firist da aka naɗa yă miƙa baye-baye da hadayu, haka ma wannan ya bukaci yă kasance da abin da zai miƙa.
Tout grand-prêtre est institué pour offrir des dons et des sacrifices; il faut donc que celui-là ait aussi quelque chose à offrir.
4 Da a ce yana a duniya ne, da bai zama firist ba, domin a nan akwai mutanen da doka ta naɗa don su miƙa baye-baye.
S'il était sur la terre, il ne serait pas même prêtre — (puisqu'il s'y trouve ceux qui offrent les dons selon la Loi
5 Suna hidima a cikin tsattsarkan wuri wanda yake hoto da kuma siffar abin da yake cikin sama. Shi ya sa aka gargaɗi Musa sa’ad da yana dab da gina tabanakul cewa, “Ka lura fa, ka yi kome daidai bisa ga zānen da aka nuna maka a kan dutsen.”
et qui servent ce qui n'est que la copie, l'ombre des réalités célestes, d'après l'avis donné à Moïse lorsqu'il allait dresser le tabernacle: Aie soin, lui fut-il dit, de tout faire d'après le modèle qui t'a été montré sur la montagne»),
6 Amma hidimar da Yesu ya karɓa tana da fifiko a kan tasu, kamar yadda alkawarin da shi ne yake matsakanci ya fi na dā fifiko nesa, an kuma kafa shi a kan alkawura mafi kyau.
mais il a maintenant obtenu un ministère d'autant supérieur qu'il est médiateur d'une plus excellente Alliance dont la promulgation repose sur de meilleures promesses.
7 Gama da a ce alkawari na fari ba shi da wani laifi, da ba sai an sāke neman wani ba.
En effet, si la première Alliance avait été irréprochable, il n'aurait pas été question de la remplacer par une seconde.
8 Amma Allah ya sami mutane da laifi ya ce, “Ina gaya muku lokaci yana zuwa, sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Or c'est bien un reproche qu'il fait quand il dit: «Voici qu'il vient des jours, dit le Seigneur, Où je contracterai avec la maison d'Israël et avec la maison de Juda, Une nouvelle Alliance.
9 Ba zai zama kamar irin alkawarin da na yi da kakanni-kakanninsu sa’ad da na kama hannunsu don in fitar da su daga Masar ba, domin ba su yi aminci da alkawarina ba, sai na juya musu baya, in ji Ubangiji.
Elle ne ressemblera pas à l'Alliance que je fis avec leurs pères Le jour où je les pris par la main Pour les faire sortir du pays d'Égypte; Comme ils ne sont pas restés fidèles à mon Alliance, Moi, de mon côté, je les ai négligés, dit le Seigneur.
10 Wannan shi ne alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila, bayan lokacin nan, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu. Zan zama Allahnsu, su kuwa za su zama mutanena.
Voici l'Alliance que je contracterai avec la maison d'Israël: Après ces jours-ci Je mettrai mes lois dans leur esprit Et je les graverai dans leur coeur; Je serai leur Dieu Et ils seront mon peuple,
11 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa ba, balle mutum yă ce wa ɗan’uwansa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin dukansu za su san ni, daga ƙaraminsu zuwa babba.
Et aucun d'eux n'aura à instruire son concitoyen, Ou son frère en lui disant: «Sache qui est le Seigneur.» Car tous me connaîtront Depuis le plus petit jusqu'au plus grand
12 Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuma ƙara tuna da zunubansu ba.”
Aussi serai-je plein de miséricorde pour leurs iniquités Et ne me souviendrai-je plus de leurs péchés.»
13 Ta wurin kira wannan alkawari “sabo,” ya mai da na farin tsoho ke nan; abin da yake tsoho yana kuma daɗa tsufa, zai shuɗe nan ba da daɗewa ba.
appelant cette Alliance-là «nouvelle» il a déclaré la première vieillie; or ce qui a vieilli, ce qui est suranné est près de disparaître.

< Ibraniyawa 8 >