< Ibraniyawa 8 >
1 Abin da muke magana a nan shi ne, muna da irin wannan babban firist, wanda ya zauna a hannun dama na kursiyin Maɗaukaki a sama,
And the sum concerning the things spoken of [is]: we have such a chief priest, who did sit down at the right hand of the throne of the greatness in the heavens,
2 wanda yake hidima a cikin wuri mai tsarki, tabanakul na gaskiya wanda Ubangiji ne ya kafa, ba mutum ba.
of the holy places a servant, and of the true tabernacle, which the Lord did set up, and not man,
3 Da yake dole kowane babban firist da aka naɗa yă miƙa baye-baye da hadayu, haka ma wannan ya bukaci yă kasance da abin da zai miƙa.
for every chief priest to offer both gifts and sacrifices is appointed, whence [it is] necessary for this one to have also something that he may offer;
4 Da a ce yana a duniya ne, da bai zama firist ba, domin a nan akwai mutanen da doka ta naɗa don su miƙa baye-baye.
for if, indeed, he were upon earth, he would not be a priest — (there being the priests who are offering according to the law, the gifts,
5 Suna hidima a cikin tsattsarkan wuri wanda yake hoto da kuma siffar abin da yake cikin sama. Shi ya sa aka gargaɗi Musa sa’ad da yana dab da gina tabanakul cewa, “Ka lura fa, ka yi kome daidai bisa ga zānen da aka nuna maka a kan dutsen.”
who unto an example and shadow do serve of the heavenly things, as Moses hath been divinely warned, being about to construct the tabernacle, for 'See (saith He) thou mayest make all things according to the pattern that was shewn to thee in the mount;') —
6 Amma hidimar da Yesu ya karɓa tana da fifiko a kan tasu, kamar yadda alkawarin da shi ne yake matsakanci ya fi na dā fifiko nesa, an kuma kafa shi a kan alkawura mafi kyau.
and now he hath obtained a more excellent service, how much also of a better covenant is he mediator, which on better promises hath been sanctioned,
7 Gama da a ce alkawari na fari ba shi da wani laifi, da ba sai an sāke neman wani ba.
for if that first were faultless, a place would not have been sought for a second.
8 Amma Allah ya sami mutane da laifi ya ce, “Ina gaya muku lokaci yana zuwa, sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
For finding fault, He saith to them, 'Lo, days come, saith the Lord, and I will complete with the house of Israel, and with the house of Judah, a new covenant,
9 Ba zai zama kamar irin alkawarin da na yi da kakanni-kakanninsu sa’ad da na kama hannunsu don in fitar da su daga Masar ba, domin ba su yi aminci da alkawarina ba, sai na juya musu baya, in ji Ubangiji.
not according to the covenant that I made with their fathers, in the day of My taking [them] by their hand, to bring them out of the land of Egypt — because they did not remain in My covenant, and I did not regard them, saith the Lord, —
10 Wannan shi ne alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila, bayan lokacin nan, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu. Zan zama Allahnsu, su kuwa za su zama mutanena.
because this [is] the covenant that I will make with the house of Israel, after those days, saith the Lord, giving My laws into their mind, and upon their hearts I will write them, and I will be to them for a God, and they shall be to Me for a people;
11 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa ba, balle mutum yă ce wa ɗan’uwansa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin dukansu za su san ni, daga ƙaraminsu zuwa babba.
and they shall not teach each his neighbour, and each his brother, saying, Know thou the Lord, because they shall all know Me from the small one of them unto the great one of them,
12 Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuma ƙara tuna da zunubansu ba.”
because I will be merciful to their unrighteousness, and their sins and their lawlessnesses I will remember no more;' —
13 Ta wurin kira wannan alkawari “sabo,” ya mai da na farin tsoho ke nan; abin da yake tsoho yana kuma daɗa tsufa, zai shuɗe nan ba da daɗewa ba.
in the saying 'new,' He hath made the first old, and what doth become obsolete and is old [is] nigh disappearing.