< Ibraniyawa 7 >
1 Wannan Melkizedek sarkin Salem ne da kuma firist na Allah Mafi Ɗaukaka. Shi ne ya sadu da Ibrahim ya albarkace shi sa’ad da Ibrahim ya dawowa daga cin nasara a bisa sarakuna,
For this man, Melchizedek, King of Salem and priest of the Most High God--he who when Abraham was returning after defeating the kings met him and pronounced a blessing on him--
2 Ibrahim kuwa ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome. Ma’anar sunan Melkizedek ita ce, “sarkin adalci.” Amma da yake Salem yana nufin “salama,” shi kuma “Sarkin salama” ne.
to whom also Abraham presented a tenth part of all--being first, as his name signifies, King of righteousness, and secondly King of Salem, that is, King of peace:
3 Ba shi da mahaifi ko mahaifiya, ba shi da asali, ba shi da farko ko ƙarshe, shi dai kamar Ɗan Allah ne kuma firist ne har abada.
with no father or mother, and no record of ancestry: having neither beginning of days nor end of life, but made a type of the Son of God--this man Melchizedek remains a priest for ever.
4 Ku dubi irin girman da Melkizedek mana. Ko kakanmu Ibrahim ma ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na ganima!
Now think how great this priest-king must have been to whom Abraham the patriarch gave a tenth part of the best of the spoil.
5 Yanzu doka ta umarci zuriyar Lawi waɗanda suka zama firistoci su karɓi kashi ɗaya bisa goma daga wurin mutane, wato,’yan’uwansu, ko da yake’yan’uwansu zuriyar Ibrahim ne.
And those of the descendants of Levi who receive the priesthood are authorized by the Law to take tithes from the people, that is, from their brethren, though these have sprung from Abraham.
6 Ko da yake Melkizedek ba daga zuriyar Lawi ba ne, duk da haka Ibrahim ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na abin da yake da shi, Melkizedek kuwa ya sa masa albarka, shi da aka yi wa alkawura.
But, in this instance, one who does not trace his origin from them takes tithes from Abraham, and pronounces a blessing on him to whom the promises belong.
7 Kowa ya sani cewa na gaba shi yake sa wa na baya albarka.
And beyond all dispute it is always the inferior who is blessed by the superior.
8 Firistoci ake ba wa kashi ɗaya bisa goma na abin da mutane suke samu. Amma dukan firistoci sukan mutu, sai dai Melkizedek, kuma nassi ya ce yana da rai.
Moreover here frail mortal men receive tithes: there one receives them about whom there is evidence that he is alive.
9 Ana ma iya cewa zuriyar Lawi, mai karɓar kashi ɗaya bisa goma daga mutane, ya ba da kashi ɗaya bisa goma ta wurin Ibrahim,
And Levi too--if I may so speak--pays tithes through Abraham:
10 wannan ya kasance haka domin an haifi Lawi daga baya a iyalin Ibrahim wanda ya ba wa Melkizedek kashi ɗaya bisa goma.
for Levi was yet in the loins of his forefather when Melchizedek met Abraham.
11 Ko da yake Dokar Musa ta ce dole firistoci su kasance zuriyar Lawi, waɗannan firistoci ba su iya sa wani yă zama cikakke ba. Saboda akwai bukata wani firist kamar Melkizedek ya zo, a maimakon wani daga iyalin Haruna.
Now if the crowning blessing was attainable by means of the Levitical priesthood--for as resting on this foundation the people received the Law, to which they are still subject-- what further need was there for a Priest of a different kind to be raised up belonging to the order of Melchizedek instead of being said to belong to the order of Aaron?
12 Gama in aka canja yadda ake zaɓan firist, dole a canja Dokar ita ma.
For when the priesthood changes, a change of Law also of necessity takes place.
13 Mutumin da muke wannan zance a kai, ai, shi na wata kabila ce dabam, wadda ba wani daga kabilar da ya taɓa yin hidima a bagade.
He, however, to whom that prophecy refers is associated with a different tribe, not one member of which has anything to do with the altar.
14 Kowa ya san cewa Ubangijinmu ya fito ne daga zuriyar Yahuda ne, kuma Musa bai taɓa ce firistoci za su fito daga wannan kabila ba.
For it is undeniable that our Lord sprang from Judah, a tribe of which Moses said nothing in connection with priests.
15 Canjin nan a Dokar Allah ya ƙara fitowa fili da wani firist dabam wanda yake kamar Melkizedek ya bayyana.
And this is still more abundantly clear when we read that it is as belonging to the order of Melchizedek that a priest of a different kind is to arise,
16 Ya zama firist ne ba saboda ya cika wata ƙa’ida ta zama zuriyar Lawi ba, sai dai bisa ga ikon ran da ba a iya hallakawa.
and hold His office not in obedience to any temporary Law, but by virtue of an indestructible Life.
17 Gama nassi ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
For the words are in evidence, "Thou art a priest for ever, belonging to the order of Melchizedek." (aiōn )
18 Ta haka aka kawar da ƙa’ida marar ƙarfi da kuma marar amfani
On the one hand we have here the abrogation of an earlier code because it was weak and ineffective--
19 (gama doka ba tă mai da wani abu cikakke ba), yanzu kuwa bege mafi kyau ya ɗauki matsayinta. Ta haka kuma muka matso kusa da Allah.
for the Law brought no perfect blessing--but on the other hand we have the bringing in of a new and better hope by means of which we draw near to God.
20 Ba kuwa da rashin rantsuwa aka yi haka ba. Waɗansu sun zama firistocin ba tare da wata rantsuwa ba,
And since it was not without an oath being taken--
21 shi wannan ya zama firist ta wurin rantsuwar da Allah ya yi da ya ce masa, “Ubangiji ya rantse, ba kuwa zai canja zuciyarsa ba, ‘Kai firist ne na har abada.’” (aiōn )
for these men hold office without any oath having been taken, but He holds it attested by an oath from Him who said to Him, "The Lord has sworn and will not recall His words, Thou art a Priest for ever" -- (aiōn )
22 Saboda wannan rantsuwa, Yesu ya zama tabbacin alkawari mafi kyau.
so much the more also is the Covenant of which Jesus has become the guarantor, a better covenant.
23 To, akwai waɗannan firistoci da yawa, da yake mutuwa ta hana su cin gaba da aikin zaman firist;
And they have been appointed priests many in number, because death prevents their continuance in office:
24 amma Yesu ba zai mutu ba, don haka zai zama firist har abada. (aiōn )
but He, because He continues for ever, has a priesthood which does not pass to any successor. (aiōn )
25 Saboda haka ya iya ba da ceto gaba ɗaya ga masu zuwa wurin Allah ta wurinsa, gama kullum a raye yake saboda yă yi roƙo dominsu.
Hence too He is able to save to the uttermost those who come to God through Him, seeing that He ever lives to plead for them.
26 Irin wannan babban firist ne muke bukata, shi mai tsarki ne, marar aibi, mai tsabta, ba kamar mu masu zunubi ba sam. An ɗaukaka shi fiye da kome a sama.
Moreover we needed just such a High Priest as this--holy, guileless, undefiled, far removed from sinful men and exalted above the heavens;
27 Ba ya bukata yă yi ta miƙa hadayu kowace rana saboda zunubansa, sa’an nan saboda zunuban mutane kamar sauran firistoci. Ya miƙa hadaya sau ɗaya tak, sa’ad da ya miƙa kansa.
who, unlike other High Priests, is not under the necessity of offering up sacrifices day after day, first for His own sins, and afterwards for those of the people; for this latter thing He did once for all when He offered up Himself.
28 Gama doka takan naɗa babban firist a cikin mutane masu kāsawa; amma rantsuwar da ta zo bayan dokar, ta naɗa Ɗan, wanda aka mai da shi cikakke har abada. (aiōn )
For the Law constitutes men High Priests--men with all their infirmity--but the utterance of the oath, which came later than the Law, constitutes High Priest a Son who has been made for ever perfect. (aiōn )