< Ibraniyawa 7 >
1 Wannan Melkizedek sarkin Salem ne da kuma firist na Allah Mafi Ɗaukaka. Shi ne ya sadu da Ibrahim ya albarkace shi sa’ad da Ibrahim ya dawowa daga cin nasara a bisa sarakuna,
Now this Melchisedec was king of Salem, a priest of the most high God: and he met Abraham, when returning from the slaughter of the kings; and blessed him.
2 Ibrahim kuwa ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome. Ma’anar sunan Melkizedek ita ce, “sarkin adalci.” Amma da yake Salem yana nufin “salama,” shi kuma “Sarkin salama” ne.
And to him Abraham imparted tithes of all that he had with him. Moreover his name is interpreted king of righteousness; and again he is called King of Salem, that is King of Peace.
3 Ba shi da mahaifi ko mahaifiya, ba shi da asali, ba shi da farko ko ƙarshe, shi dai kamar Ɗan Allah ne kuma firist ne har abada.
Of whom neither his father nor his mother are written in the genealogies; nor the commencement of his days, nor the end of his life; but, after the likeness of the Son of God, his priesthood remaineth for ever.
4 Ku dubi irin girman da Melkizedek mana. Ko kakanmu Ibrahim ma ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na ganima!
And consider ye, how great he was; to whom the patriarch Abraham gave tithes and first-fruits.
5 Yanzu doka ta umarci zuriyar Lawi waɗanda suka zama firistoci su karɓi kashi ɗaya bisa goma daga wurin mutane, wato,’yan’uwansu, ko da yake’yan’uwansu zuriyar Ibrahim ne.
For they of the sons of Levi who received the priesthood, had a statute of the law, that they should take tithes from the people; they from their brethren, because they also are of the seed of Abraham.
6 Ko da yake Melkizedek ba daga zuriyar Lawi ba ne, duk da haka Ibrahim ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na abin da yake da shi, Melkizedek kuwa ya sa masa albarka, shi da aka yi wa alkawura.
But this man, who is not enrolled in their genealogies, took tithes from Abraham; and blessed him who had received the promise.
7 Kowa ya sani cewa na gaba shi yake sa wa na baya albarka.
But it is beyond controversy, that the inferior is blessed by his superior.
8 Firistoci ake ba wa kashi ɗaya bisa goma na abin da mutane suke samu. Amma dukan firistoci sukan mutu, sai dai Melkizedek, kuma nassi ya ce yana da rai.
And here, men who die, receive the tithes; but there he of whom the scripture testifieth that he liveth.
9 Ana ma iya cewa zuriyar Lawi, mai karɓar kashi ɗaya bisa goma daga mutane, ya ba da kashi ɗaya bisa goma ta wurin Ibrahim,
And through Abraham, as one may say, even Levi who receiveth tithes, was himself tithed.
10 wannan ya kasance haka domin an haifi Lawi daga baya a iyalin Ibrahim wanda ya ba wa Melkizedek kashi ɗaya bisa goma.
For he was yet in the loins of his father, when he met Melchisedec.
11 Ko da yake Dokar Musa ta ce dole firistoci su kasance zuriyar Lawi, waɗannan firistoci ba su iya sa wani yă zama cikakke ba. Saboda akwai bukata wani firist kamar Melkizedek ya zo, a maimakon wani daga iyalin Haruna.
If, therefore, perfection had been by means of the priesthood of the Levites, in which the law was enjoined on the people; why was another priest required, who should stand up after the likeness of Melchisedec? For it should have said, He shall be after the likeness of Aaron.
12 Gama in aka canja yadda ake zaɓan firist, dole a canja Dokar ita ma.
But as there is a change in the priesthood, so also is there a change in the law.
13 Mutumin da muke wannan zance a kai, ai, shi na wata kabila ce dabam, wadda ba wani daga kabilar da ya taɓa yin hidima a bagade.
For he of whom these things were spoken, was born of another tribe, of which no one ever ministered at the altar.
14 Kowa ya san cewa Ubangijinmu ya fito ne daga zuriyar Yahuda ne, kuma Musa bai taɓa ce firistoci za su fito daga wannan kabila ba.
For it is manifest that our Lord arose from Judah, from a tribe of which Moses said nothing concerning a priesthood.
15 Canjin nan a Dokar Allah ya ƙara fitowa fili da wani firist dabam wanda yake kamar Melkizedek ya bayyana.
And moreover this is further manifest, from his saying that another priest will stand up, after the likeness of Melchisedec,
16 Ya zama firist ne ba saboda ya cika wata ƙa’ida ta zama zuriyar Lawi ba, sai dai bisa ga ikon ran da ba a iya hallakawa.
who was not according to the law of corporeal injunctions, but according to the energy of an indissoluble life.
17 Gama nassi ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn )
For he testified of him: Thou art a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
18 Ta haka aka kawar da ƙa’ida marar ƙarfi da kuma marar amfani
And the change which was made in the first statute, was on account of its impotency, and because their was no utility in it.
19 (gama doka ba tă mai da wani abu cikakke ba), yanzu kuwa bege mafi kyau ya ɗauki matsayinta. Ta haka kuma muka matso kusa da Allah.
For the law perfected nothing; but in the place of it there came in a hope, which is better than it, and by which we draw near to God.
20 Ba kuwa da rashin rantsuwa aka yi haka ba. Waɗansu sun zama firistocin ba tare da wata rantsuwa ba,
And he confirmed it to us by an oath.
21 shi wannan ya zama firist ta wurin rantsuwar da Allah ya yi da ya ce masa, “Ubangiji ya rantse, ba kuwa zai canja zuciyarsa ba, ‘Kai firist ne na har abada.’” (aiōn )
For they became priests without an oath; but this man by an oath. As he said to him by David: The Lord hath sworn, and will not lie, Thou art a priest for ever, after the likeness of Melchisedec. (aiōn )
22 Saboda wannan rantsuwa, Yesu ya zama tabbacin alkawari mafi kyau.
By all this, is that a better covenant of which Jesus is the sponsor.
23 To, akwai waɗannan firistoci da yawa, da yake mutuwa ta hana su cin gaba da aikin zaman firist;
And they as priests were numerous, because they were mortal, and were not permitted to continue:
24 amma Yesu ba zai mutu ba, don haka zai zama firist har abada. (aiōn )
but this man, because he standeth up for ever, his priesthood doth not pass away: (aiōn )
25 Saboda haka ya iya ba da ceto gaba ɗaya ga masu zuwa wurin Allah ta wurinsa, gama kullum a raye yake saboda yă yi roƙo dominsu.
and he is able to vivify for ever, them who come to God by him; for he always liveth, and sendeth up prayers for them.
26 Irin wannan babban firist ne muke bukata, shi mai tsarki ne, marar aibi, mai tsabta, ba kamar mu masu zunubi ba sam. An ɗaukaka shi fiye da kome a sama.
For, a priest like to him, was also suitable for us; one pure, and without evil and without stain; one separated from sins, and exalted higher than heaven;
27 Ba ya bukata yă yi ta miƙa hadayu kowace rana saboda zunubansa, sa’an nan saboda zunuban mutane kamar sauran firistoci. Ya miƙa hadaya sau ɗaya tak, sa’ad da ya miƙa kansa.
and who is not obliged, every day, like the Aaronic high priest, to first offer sacrifices for his own sins, and then for the people; for this he did once, by offering up himself.
28 Gama doka takan naɗa babban firist a cikin mutane masu kāsawa; amma rantsuwar da ta zo bayan dokar, ta naɗa Ɗan, wanda aka mai da shi cikakke har abada. (aiōn )
For the law constituted feeble men priests; but the word of the oath, which was subsequent to the law constituted the Son perfect for ever. (aiōn )