< Ibraniyawa 6 >
1 Dole mu yi ƙoƙarin zama balagaggu mu kuma fara tunani game da abubuwan da suka fi koyarwan nan mai sauƙi game da Kiristi. Bai kamata mu ci gaba da magana game da me ya sa dole mu juye daga ayyukan da suke kawo mutuwa da kuma me ya sa za mu kasance da bangaskiya a cikin Allah ba.
Dlatego zostawmy podstawowe nauki o Chrystusie i przejdźmy do tego, co doskonałe, nie zakładając ponownie fundamentu, [którym jest] pokuta od martwych uczynków i wiara w Boga;
2 Kuma bai kamata mu ci gaba da koyar da umarnai game da baftisma, ɗibiya hannuwa, tashin matattu, da kuma madawwamin hukunci ba. (aiōnios )
Nauka o chrztach i nakładaniu rąk, o zmartwychwstaniu umarłych i sądzie wiecznym. (aiōnios )
3 Da yardar Allah, za mu ci gaba ga ƙarin ganewa.
I to uczynimy, jeśli Bóg pozwoli.
4 Waɗanda suka taɓa samun haske, waɗanda suka ɗanɗana kyauta ta sama, waɗanda suka sami rabo cikin Ruhu Mai Tsarki,
Niemożliwe jest bowiem, żeby tych, którzy raz zostali oświeceni i zakosztowali daru niebieskiego, i stali się uczestnikami Ducha Świętego;
5 waɗanda suka ɗanɗana daɗin maganar Allah da kuma ikokin zamani mai zuwa, (aiōn )
Zakosztowali też dobrego słowa Bożego i mocy przyszłego wieku; (aiōn )
6 ba ya yiwuwa a sāke kawo su ga tuba in suka kauce, domin suna sāke gicciye Ɗan Allah ke nan suna kuma kunyata shi a gaban jama’a.
A odpadli – ponownie odnowić ku pokucie, gdyż sami sobie znowu krzyżują Syna Bożego i wystawiają go na hańbę.
7 Ƙasar da take shan ruwan sama da yake fāɗi a kanta kullum da kuma take ba da hatsin da yake da amfani ga waɗanda ake noma dominsu, takan sami albarkar Allah.
Ziemia bowiem, która pije deszcz często na nią spadający i rodzi rośliny użyteczne dla tych, którzy ją uprawiają, otrzymuje błogosławieństwo od Boga.
8 Amma ƙasar da take ba da ƙaya da sarƙaƙƙiya ba ta da amfani tana kuma cikin hatsarin la’ana. A ƙarshe za a ƙone ta.
Lecz ta, która wydaje ciernie i osty, jest odrzucona i bliska przekleństwa, a jej końcem [jest] spalenie.
9 Abokaina, ko da yake muna irin maganan nan, mun tabbata kuna yi abubuwan nan masu kyau da waɗanda suka sami ceto suke yi.
Ale chociaż tak mówimy, umiłowani, jesteśmy co do was przekonani o czymś lepszym i towarzyszącym zbawieniu.
10 Allah ba marar adalci ba ne. Ba zai manta da aikinku da kuma ƙaunar da kuka nuna masa wajen taimakon mutanensa da kuma ci gaba da taimakonsu da kuke yi ba.
Bóg bowiem nie jest niesprawiedliwy, aby miał zapomnieć o waszym dziele i trudzie miłości, którą okazaliście dla jego imienia, gdy służyliście świętym i [nadal] służycie.
11 Muna so kowannenku yă nuna ƙwazon nan har zuwa ƙarshe, domin ku tabbatar da begenku.
Pragniemy zaś, aby każdy z was okazywał tę samą gorliwość, żebyście [mieli] pełnię nadziei aż do końca;
12 Ba ma so ku zama masu ƙyuya, sai dai ku yi koyi da waɗanda ta wurin bangaskiya da haƙuri suka gāji abin da aka yi alkawari.
Abyście nie byli ociężali, ale naśladowali tych, którzy przez wiarę i cierpliwość dziedziczą obietnice.
13 Babu wanda ya fi Allah, saboda haka sa’ad da ya yi alkawari ga Ibrahim, sai ya rantse da sunansa,
Gdy bowiem Bóg dał obietnicę Abrahamowi, a nie miał nikogo większego, na kogo mógłby przysiąc, przysiągł na siebie samego;
14 cewa, “Tabbatacce zan albarkace ka in kuma ba ka zuriya mai yawa.”
Mówiąc: Zaprawdę, błogosławiąc, błogosławić ci będę i rozmnażając, rozmnożę cię.
15 Haka kuwa bayan Ibrahim ya jira da haƙuri, sai ya karɓi abin da aka yi alkawari.
A ponieważ tak cierpliwie czekał, dostąpił [spełnienia] obietnicy.
16 In mutane za su yi rantsuwa sukan yi haka da wanda ya fi su ne, rantsuwar kuwa takan tabbatar da abin da aka faɗa ta kuma kawo ƙarshen dukan gardama.
Ludzie bowiem przysięgają na kogoś większego, a przysięga dla potwierdzenia jest zakończeniem wszystkich sporów między nimi.
17 Saboda haka da Allah ya so yă bayyana nufinsa marar canjawa a sarari ga magādan abin da aka yi alkawari, sai ya tabbatar da shi da rantsuwa.
Dlatego też Bóg, chcąc dobitniej okazać dziedzicom obietnicy niezmienność swojego postanowienia, poręczył ją przysięgą;
18 Allah ba ya karya! Haka ma alkawuransa da rantsuwarsa abubuwa biyu ne da ba a iya canjawa. Mun gudu zuwa wurin Allah domin kāriya. Ya kamata alkawuransa su ƙarfafawa sosai mu riƙe begen nan da yake gabanmu.
Abyśmy przez dwie niezmienne rzeczy, w których jest niemożliwe, aby Bóg kłamał, mieli silną pociechę, [my], którzy uciekliśmy, by pochwycić się zaoferowanej nam nadziei;
19 Muna da wannan bege kamar anka na rai, kafaffe da kuma tabbatacce. Yana shiga tsattsarkan wuri na can ciki a bayan labule,
Którą mamy jako kotwicę duszy, bezpieczną i niewzruszoną, sięgającą poza zasłonę;
20 inda Yesu, wanda ya sha gabanmu, ya shiga a madadinmu. Ya zama babban firist na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek. (aiōn )
Gdzie [jako] poprzednik wszedł dla nas Jezus, stawszy się najwyższym kapłanem na wieki według porządku Melchizedeka. (aiōn )