< Ibraniyawa 5 >

1 Akan zaɓi kowane babban firist daga cikin mutane ne, akan kuma naɗa shi domin yă wakilce su a kan al’amuran Allah, domin yă miƙa kyautai da hadayu saboda zunubai.
Förty hvar och en öfverste Prest, den af menniskom uttags, han varder satt för menniskorna, i de ting som Gudi på röra, att han skall offra gåfvor och offer för synderna.
2 Da yake babban firist ɗin mai kāsawa ne, yana iya bin da jahilai da kuma waɗanda suka kauce hanya, a hankali.
Den der kan varkunna sig öfver dem, som fåkunnige äro och ville fara; efter han är ock sjelf belagd med svaghet.
3 Shi ya sa dole yă miƙa hadayu domin zunubansa, da kuma domin zunuban mutane.
Derföre måste han ock, såsom för folket, så ock för sig sjelf offra, för synder.
4 Ba wanda yakan kai kansa a wannan matsayi mai girma; sai ko Allah ya kira shi, kamar yadda aka yi wa Haruna.
Och ingen tager sig sjelf äro; utan den som ock kallad varder af Gudi, lika som Aaron.
5 Haka ma Kiristi bai kai kansa neman ɗaukaka na zama babban firist ba. Allah ne dai ya ce masa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka.”
Så hafver ock icke Christus gjort sig sjelf härligan, att han skulle varda öfverste Prest; utan den, som sade till honom: Du äst min Son, i dag hafver jag födt dig;
6 Ya kuma ya ce a wani wuri, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn g165)
Såsom han ock annorstäds säger: Du äst en Prest i evig tid, efter Melchisedeks sätt; (aiōn g165)
7 A lokacin da Yesu ya yi rayuwa a duniya, ya yi addu’o’i da roƙe-roƙe tare da kuka mai zafi da kuma hawaye ga wannan wanda yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa ji shi saboda tsananin bangirman da ya yi.
Och hafver på sins kötts dagar offrat bön och åkallan, med starkt rop och tårar till honom, som honom frälsa kunde ifrå döden; och vardt bönhörd, derföre att han höll Gud i vördning.
8 Ko da yake shi ɗa ne, ya yi biyayya ta wurin shan wahala
Och ändå han var Guds Son, hafver han dock af thy han led lärt lydno.
9 kuma da aka mai da shi cikakke, sai ya zama hanyar samun madawwamin ceto ga dukan waɗanda suke masa biyayya. (aiōnios g166)
Och då han fullkommen vardt, blef han allom dem, som honom lyda, en orsak till evig salighet; (aiōnios g166)
10 Allah kuwa ya naɗa shi yă zama babban firist, bisa ga tsarin Melkizedek.
Kallad af Gudi en öfverste Prest, efter Melchisedeks sätt.
11 Muna da abubuwa masu yawa da za mu faɗa game da wannan batu, sai dai yana da wuya a bayyana, da yake ba ku da saurin ganewa.
Derom vi hade väl mycket tala; men det är svårt, efter I ären så oförståndige;
12 Gaskiya, a yanzu ya kamata a ce kun zama malamai, sai ga shi kuna bukatar wani yă sāke koya muku abubuwa masu sauƙi game da abin da Allah ya faɗa. Kuna bukatar madara, ba abinci mai kauri ba!
Och I, som längesedan skulle varit lärare, behöfven åter att man lärer eder de första bokstäfverna af Guds ord; och att man gifver eder mjölk, och icke stadig mat.
13 Duk wanda yake rayuwa a kan madara, shi kamar jariri ne har yanzu, kuma bai san ainihi mene ne ya dace ba.
Ty hvem man ännu mjölk gifva måste, han är oförfaren i rättfärdighetenes ord; ty han är ett barn.
14 Amma abinci mai kauri na balagaggu ne, waɗanda suka hori kansu don su bambanta tsakanin nagarta da mugunta.
Men dem, som fullkomne äro, tillhörer stadig mat, de som genom vanan öfvade äro i sinnen, till att åtskilja godt och ondt.

< Ibraniyawa 5 >