< Ibraniyawa 5 >

1 Akan zaɓi kowane babban firist daga cikin mutane ne, akan kuma naɗa shi domin yă wakilce su a kan al’amuran Allah, domin yă miƙa kyautai da hadayu saboda zunubai.
For every hye prest that is taken from amoge men is ordeyned for men in thynges pertaynynge to god: to offer gyftes and sacryfyses for synne:
2 Da yake babban firist ɗin mai kāsawa ne, yana iya bin da jahilai da kuma waɗanda suka kauce hanya, a hankali.
which can have compassion on the ignoraunt and on them that are out of the waye because that he him silfe also is compased with infirmitie:
3 Shi ya sa dole yă miƙa hadayu domin zunubansa, da kuma domin zunuban mutane.
For the which infirmities sake he is bounde to offer for synnes as well for hys awne parte as for the peoples.
4 Ba wanda yakan kai kansa a wannan matsayi mai girma; sai ko Allah ya kira shi, kamar yadda aka yi wa Haruna.
And no man taketh honour vnto him silfe but he that is called of God as was Aaron.
5 Haka ma Kiristi bai kai kansa neman ɗaukaka na zama babban firist ba. Allah ne dai ya ce masa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka.”
Even so lykewise Christ glorified not him silfe to be made the hye prest: but he that sayde vnto him: thou arte my sonne this daye begat I the glorified him.
6 Ya kuma ya ce a wani wuri, “Kai firist ne na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.” (aiōn g165)
As he also in another place speaketh: Thou arte a prest for ever after the order of Melchisedech. (aiōn g165)
7 A lokacin da Yesu ya yi rayuwa a duniya, ya yi addu’o’i da roƙe-roƙe tare da kuka mai zafi da kuma hawaye ga wannan wanda yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa ji shi saboda tsananin bangirman da ya yi.
Which in the dayes of his flesshe did offer vp prayers and sup plicacions with stronge cryinge and teares vnto him that was able to save him from deeth: and was also hearde because of his godlines.
8 Ko da yake shi ɗa ne, ya yi biyayya ta wurin shan wahala
And though he were Goddes sonne yet learned he obediece by tho thynges which he suffered
9 kuma da aka mai da shi cikakke, sai ya zama hanyar samun madawwamin ceto ga dukan waɗanda suke masa biyayya. (aiōnios g166)
and was made parfaite and the cause of eternall saluacion vnto all them that obey him: (aiōnios g166)
10 Allah kuwa ya naɗa shi yă zama babban firist, bisa ga tsarin Melkizedek.
and is called of God an hye prest after the order of Melchisedech.
11 Muna da abubuwa masu yawa da za mu faɗa game da wannan batu, sai dai yana da wuya a bayyana, da yake ba ku da saurin ganewa.
Wherof we have many thynges to saye which are harde to be vttered: because ye are dull of hearinge.
12 Gaskiya, a yanzu ya kamata a ce kun zama malamai, sai ga shi kuna bukatar wani yă sāke koya muku abubuwa masu sauƙi game da abin da Allah ya faɗa. Kuna bukatar madara, ba abinci mai kauri ba!
For when as cocerninge ye tyme ye ought to be teachers yet have ye nede agayne that we teache you the fyrst principles of the worde of god: and are become soche as have nede of mylke and not of stronge meate:
13 Duk wanda yake rayuwa a kan madara, shi kamar jariri ne har yanzu, kuma bai san ainihi mene ne ya dace ba.
For every man that is feed with mylke is inexperte in the worde of rightewesnes. For he is but a babe.
14 Amma abinci mai kauri na balagaggu ne, waɗanda suka hori kansu don su bambanta tsakanin nagarta da mugunta.
But stronge meate belongeth to them that are parfecte which thorow custome have their wittes exercised to iudge both good and evyll also.

< Ibraniyawa 5 >