< Ibraniyawa 4 >
1 Saboda haka, da yake alkawarin shiga hutunsa yana nan har yanzu, sai mu yi hankali kada waninku yă kāsa shiga.
Lader os derfor, da der endnu står en Forjættelse tilbage om at indgå til hans Hvile, vogte os for, at nogen af eder skal mene, at han er kommen for silde.
2 Gama mu ma mun ji an yi mana wa’azin bishara, kamar yadda su ma suka ji; sai dai saƙon da suka ji ba tă amfane su ba, domin waɗanda suka ji ba su karɓe shi da bangaskiya ba.
Thi også os er der forkyndt godt Budskab ligesom hine; men Ordet, som de hørte, hjalp ikke dem, fordi det ikke var forenet med Troen hos dem, som hørte det.
3 Mu kam da muka gaskata mu ne muka shiga wannan hutu, kamar yadda Allah ya ce, “Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’” Allah ya faɗa haka ko da yake ya riga ya kammala aikinsa tun halittar duniya.
Thi vi gå ind til Hvilen, vi, som ere komne til Troen, efter hvad han har sagt: "Så svor jeg i min Vrede: Sandelig, de skulle ikke gå ind til min Hvile", omendskønt Gerningerne vare fuldbragte fra Verdens Grundlæggelse.
4 Gama a wani wuri ya yi magana a kan rana ta bakwai cikin waɗannan kalmomi, “A rana ta bakwai kuwa Allah ya huta daga dukan aikinsa.”
Thi han har et Sted sagt om den syvende Dag således: "Og Gud hvilede på den syvende Dag fra alle sine Gerninger."
5 Haka kuma a nassin nan ya ce, “Ba za su taɓa shiga hutuna ba.”
Og fremdeles på dette Sted: "Sandelig, de skulle ikke gå ind til min Hvile."
6 Har yanzu dai da sauran dama domin waɗansu su shiga, su kuwa waɗanda aka fara yi wa albishirin nan sun kāsa shiga saboda rashin biyayya.
Efterdi der altså står tilbage, at nogle skulle gå ind til den, og de, hvem der først blev forkyndt godt Budskab, ikke gik ind for deres Genstridigheds Skyld:
7 Saboda haka Allah ya sāke sa wata rana, yana kiranta Yau, bayan wani dogon lokaci Allah ya yi magana ta bakin Dawuda, yadda aka riga aka faɗa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku.”
så bestemmer han atter en Dag: "I Dag", siger han ved David så lang Tid efter, (som ovenfor sagt): "I Dag, når I høre hans Røst, da forhærder ikke eders Hjerter!"
8 Gama da a ce Yoshuwa ya ba su hutu, da Allah bai yi magana daga baya a kan wata rana dabam ba.
Thi dersom Josva havde skaffet dem Hvile, da vilde han ikke tale om en anden Dag siden efter.
9 Har yanzu, akwai wani hutun Asabbacin da ya rage domin mutanen Allah;
Altså er der en Sabbatshvile tilbage for Guds Folk.
10 gama duk wanda ya shiga hutun Allah, shi ma yakan huta daga nasa aiki, kamar yadda Allah ya huta daga nasa.
Thi den, som er gået ind til hans Hvile, også han har fået Hvile fra sine Gerninger, ligesom Gud fra sine.
11 Saboda haka, bari mu yi iyakacin ƙoƙarinmu mu shiga wannan hutu, don kada wani yă kāsa ta wurin bin gurbinsu na rashin biyayya.
Lader os derfor gøre os Flid for at gå ind til hin Hvile, for at ikke nogen skal falde ved den samme Genstridighed, som hine gave Eksempel på.
12 Maganar Allah tana da rai, tana kuma da ƙarfin aiki. Ta fi kowane takobi mai baki biyu kaifi. Maganarsa takan ratsa har ciki-ciki, tana raba rai da ruhu, gaɓoɓi da kuma ɓargon ƙashi; har sai ta tone ainihi wane ne muke.
Thi Guds Ord er levende og kraftigt og skarpere end noget tveægget Sværd og trænger igennem, indtil det deler Sjæl og Ånd, Ledemod såvel som Marv, og dømmer over Hjertets Tanker og Råd.
13 Babu wani abu cikin dukan halittar da yake ɓoye daga fuskar Allah. Kowane abu a buɗe yake yana kuma a shimfiɗe a idanun wanda dole mu ba da lissafi a gare shi.
Og ingen Skabning er usynlig for hans Åsyn; men alle Ting ere nøgne og udspændte for hans Øjne, hvem vi stå til Regnskab.
14 Saboda haka, da yake muna da babban firist mai girma wanda ya ratsa sama, Yesu Ɗan Allah, bari mu riƙe bangaskiyan nan wadda muke shaidawa da ƙarfi.
Efterdi vi altså have en stor Ypperstepræst, som er gået igennem Himlene, Jesus, Guds Søn, da lader os holde fast ved Bekendelsen!
15 Gama babban firist da muke da shi ba marar juyayin kāsawarmu ba ne, amma muna da wanda aka gwada ta kowace hanya, kamar dai yadda akan yi mana, duk da haka bai yi zunubi ba.
Thi vi have ikke en Ypperstepræst, som ej kan have Medlidenhed med vore Skrøbeligheder, men en sådan, som er fristet i alle Ting i Lighed med os, dog uden Synd.
16 Saboda haka sai mu matso kusa da kursiyin alheri da ƙarfi zuciya, don mu sami jinƙai mu kuma sami alherin da zai taimake mu a lokacin bukata.
Derfor lader os træde frem med Frimodighed for Nådens Trone, for at vi kunne få Barmhjertighed og finde Nåde til betimelig Hjælp.