< Ibraniyawa 3 >

1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Lino, vanyalukolo vimike, vahangi va ng'emelo sa vulanga, munsaghe u Yesu, vasung'ua nu n'tekesi um'baha vupoki vwitu.
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
Ulwakuva alyale n'kola kwa Nguluve juno alya nsalwile, ndavule alyale n'kola uMusa kange munymba joni ija Nguluve.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
Ulwkuva u Yesu avalilue kuva nu vwoghopua uvuvaha kukila vuno alyalenavo uMusa, ulwakuva jula juno ajengile inyumba alimukivalilo kya vwoghopua kukila inyuma jijio.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
Ulwakuva inyumba jejoni jijengua nu muunhu jumonga, looli juno ijenga ifinu fyoni ghwe Nguluve.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
Sakyang'ani uMusa alyale mitike ndavule um'bombi mu nyumba joni ija Nguluve, yevihumia uvwolesi vwimila amasio ghano ghilijovua unsinki ghuno ghulikwisa.
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
Looli u Kilisite Mwana ghwa Nguluve mu vwimilisi vwa nyumba ija Nguve. Usue tuli nyumba jamwene nave tukola ng'aning'ani mu vwitiki na mulutogo vwitika.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Pa uluo, pe hwene uMhepo u Mwimike vule ijova, “Umusyughu, nave ghupulika ilisio lya mwene,
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
Ulajbikagha inumbula jako kuva nalamu ndavule ava Israeli vule vakavombile uvuvwafu, mu nsiki ughwa kughelua mu fidunda.
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
Unsiki ughuno ava nhaata viinhu vakanikuvisie mungelo, nu nsiki, ghwa maka fijigho fine, vakasagha imbombo sango.
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
Pa uluo nanikakelile ni kikolo ikio. Nikajova, “Visova unsiki ghoni mu moojo ghave navakagwile isila sango.
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Hwene vule nika jighile mu lyoojo lyango: navikwingila ulutogo lwango.”
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Muve maso, vanyalukolo, kuti nakweghungavisaghe umwojo umosi ghuno naghukwitika muvamo vini, inumbula jino jiva kutali nu Nguluve juno mwumi.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
Pauluo, mupulisiaghe ifighono fyoni umuunhu ghweni nu nine, neke pano kitambulua ikighono munogheluaghe, neke jumonga mulyumue alekaghe piva nsila vuhugu kuvu syangi vwa nyivi.
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
Ulwakuva tuli vahangilanisi va Kilisite tungave nuvumo nuvuvoneng'ano vwitu ku ngufu mwa mwene kuhumia amasaghe kufika kuvusililo.
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
Vwimila vwa iili ye lijovilue, “Umusyughu nave mupulika ilisio lyamwene, mulabika amoojo ghinu ghave ghasila vuhugu, ndavule ava Israeli vuli vakavombile unsiki ghwa vuhosi.”
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
Vevaveni avuo vano vampulike u Nguluve kuvuhosi? Navalyale vevala vono uMusa akavongelisie kuhuma ku Misri?
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
Vevaveni vano uNguluve akavakalalile mu maka fijigho fine? Kisila vumo vwaa vala vano vakavombile inyivi, vano amavili ghuvanave ghalyafwile ghalyaghonile mulukuve?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
Vevaveni vano vakafingile uNguluve kuti navilikwingila mulutogo lwa mwene, nave navevala vano vakamwitike umwene?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
Tuvona ulwakuti navakaghwesisie kukwingila mulutogo lwa mwene ulwakuva navakitike.

< Ibraniyawa 3 >