< Ibraniyawa 3 >

1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Тому, святі брати, учасники небесного покликання, дивіться на Апостола та Первосвященника нашого свідчення – Ісуса.
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
Він був вірний Тому, Хто призначив Його, як і Мойсей був вірний в усьому [Божому] домі.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
Але [Ісус] гідний більшої шани, ніж Мойсей, як і будівельник має більшу честь, ніж сам дім.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
Бо всякий дім хтось збудував, а Той, Хто збудував усе, – Бог.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
Мойсей був вірним слугою в усьому домі [Божому], щоб свідчити про те, що буде сказано в майбутньому.
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
А Христос – [вірний] Син над домом [Божим]. І Його дім – ми, якщо будемо й далі непохитно триматися сміливості та надії, якою ми пишаємося.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Отже, як каже Святий Дух: «Сьогодні, коли ви почуєте Його голос,
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
не зачерствійте серцями вашими, як було в [день] повстання, у день випробування в пустелі,
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
де Мене спокушали ваші батьки, випробовуючи Мене, хоча й бачили Мої діла
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
сорок років. Тоді Я обурився на цей рід і сказав: „Вони завжди блукають своїм серцем, не знають шляхів Моїх.
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Тому присягнув Я у гніві Моєму: не увійдуть вони до Мого спокою!“».
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Стережіться, брати, щоб ні в кого з вас не було лукавого та невірного серця, що призведе до відвернення від живого Бога.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
Але підбадьорюйте одне одного щодня, доки це «сьогодні» ще триває, щоб ніхто з вас не зачерствів через оману гріха.
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
Адже ми стали учасниками Христа, якщо лише твердо збережемо до кінця [нашу] первісну надію.
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
Як сказано: «Сьогодні, якщо ви почуєте Його голос, не зачерствійте серцями вашими, як було в [день] повстання».
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
Бо ким були ті, що, почувши [голос Божий], збунтувалися? Чи не всі ті, що вийшли з Єгипту з Мойсеєм?
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
А на кого Він гнівався сорок років? Хіба не на тих, хто згрішив, чиї тіла загинули в пустелі?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
І кому [Бог] поклявся, що не ввійдуть до Його спокою, як не тим, хто не послухався?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
Тож, як бачимо, вони не змогли увійти через невіру.

< Ibraniyawa 3 >